الثلاثاء، أبريل 19، 2011


Nuhu Ribadu

Nuhu Ribadu ya yi alkawarin kafa sabuwar Najeriya


An haifi Malam Nuhu Ribadu a ranar 21 ga watan Nuwamban 1960.


Ya samu shaidar digiri ta farko a fannin ilimin shari'a daga jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a 1983.


Ya kuma karbi shaidarsa ta zama lauya a shekara ta 1984.


Malam Nuhu Ribadu ya kara halartar jami'ar Ahmadu Bello domin karatun digiri na biyu a fannin na shari'a.


Sannan ya halarci sashin kasuwanci na jami'ar Harvard da ke Amurka.


Daga nan ne kuma ya fara aiki da Hukumar 'yan sandan Najeriya, inda ya ci gaba da aiki a matakai daban-daban, har ya zamo shugaban bangaren shari'a da gabatar da masu laifi a ofishin Hukumar da ke Abuja.


Shekaru 18 din da ya shafe yana aiki a Hukumar 'yan sandan Najeriya, ya kai har aka nada shi shugaban Hukumar yaki da yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati (EFCC) a watan Afrilun shekara ta 2003.


Yana cikin kwamitin tattalin arziki da shugaba Obasanjo ya kafa a shekara ta 2003 zuwa 2008, wanda ya haifar da sauye-sauyen da aka gudanar a bangarori daban daban na kasar.



Malam Nuhu ya bayyana aniyarsa ta tsaya wa takarar shugaban kasa a zaben da za a yi a watan Afrilu karkashin jam'iyyar adawa ta ACN a a watan Disambar 20101



Nasarar da ya samu ta hadar da cire Najeriya daga jerin kasashen da ba sa bada hadin kai ta fuskar yaki da cin hanci da rashawa.


A watan Oktoban 2007 ne kuma tsohuwar gwamnatin shugaba Umaru 'Yaradua ta cire shi daga shugabancin Hukumar ta EFCC, sannan aka tura shi ya karo karatu.


Mallam Ibrahim Shekarau



An haifi Shekarau ne a unguwar Kurmawa da ke jihar Kano, Ya kuma yi karatun Firamare a makarantar Gidan Makama daga shekarar (1961-1967).


Ya yi karantun sakandare a Kano Commercial College daga shekarar (1967-1973) sannan kuma ya garzaya jam'iyyar Ahmadu Bello da ke Zaria daga shekarar (1973-1977) inda ya samu takardar shaidar digiri ta farko.


Bayan da ya kammala karatunsa na jami'a, mallam Ibrahim Shekarau ya yi aikin gwamnati, sannan ya koma dakin karatu inda ya zama malamin lissafi a Government Technical College da ke Wudil a shekarar 1978, bayan shekaru biyu ne kuma ya zama shugaban makarantar Government Day Junior Secondary School a Wudil.


A shekarar 1980 an koma da shi makarantar Government Secondary School da ke Hadejia, sannan Government College Birnin Kudu a 1986, sai kuma Government Secondary School a Gwammaja da kuma makarantar Rumfa College a 1988, duk a matsayin shugaban makaranta.


Daga nana dai mallam Shekarau ya zama mataimakin darakta a harkar illimi a shekarar 1992, bayan kuma shekara guda aka mayar da shi darekta.


Daga nan dai likkafa ta ci gaba inda ya zama babban sakatare a ma'ikatar harkar illimi.


A watan Fabrerun shekarar 2000, malam Shekarau ya koma aikin gwamnati, kafin a koma da shi kwalejin share fagen shiga jam'ia a matsayin babban malamin lissafi.


A nan dai Shekarau ya ajiye aiki da gwamnati bayan ya yi aikin na tsawon watanni 17 a kwalejin.


Siyasa


Ba'a dauki Malam Ibrahim Shekarau a matsayin wani dan takara da zai yi tasiri ba a zaben gwamnan da aka yi a shekarar 2003 a jihar, amma daga baya kuma sai ya yi tasiri inda ya lashe zaben.


Kuma Malam shekarau ya kafa tarihi inda ya zama gwamna na farko da aka zabe shi a karo na biyu a matsayin gwamna a jihar Kano.


Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero, ya nada shi a matsayin Sardaunan Kano a karon farko a tarihin masauratar Kano.


Malam Ibrahim Shekaru ne dai dan takarar shugaban kasa, karkashin inuwar jam'iyar ANPP a Zaben watan Afrilu na shekarar 2011.

Takaitaccen tarihin janar Mohammadu Buhari

Janar Mohammadu Buhari







dansudan

An haifi Janar Muhammadu Buhari ranar 17 ga watan Disambar shekarar 1942, a garin Daura.
Tauraruwar janar Buhari ta fara haskawa a lokacin da aka bashi mukamin ministan man petur da ma'adanai a shekarar 1975, a zamanin mulkin sojin janar Olusegun Obasanjo.
Ko da yake kafin nan shi ne gwamnan sabuwar jahar Arewa maso Gabas da janar Murtala Ramat Muhammed ya kirkiro.
Daga bisani kuma aka nada shi shugaban hukumar NNPC wadda aka fara kafawa a shekarar 1977.
A zamanin mulkin Janar Sani Abacha an nada shi shugaban hukumar PTF wadda aka kafa da kudaden rarar man da kasar ta samu a wannan lokaci domin gudanar da ayyukan ci gaban al'umma.
Kuma ayyukan da janar Buhari yayi wa Najeriya kama daga hanyoyi, asibitoci zuwa makarantu yasa wasu 'yan Najeriya son ganin ya sake zama shugaban kasar.
Sau biyu janar Muhammdu Buhari yana tsayawa takarar shugaban kasar karkashin tutar jam'iyyar ANPP wato 2003 da 2007, wadanda duka bai samu nasara ba.
Rashin nasarar da ya yi karo biyu bai sauya masa ra'ayi ba game da siyasa a Najeriya, kuma tuni ya kaddamar da tashi jam'iyyar da ya kira CPC wadda yake takarar shugaban kasa a zaben da za'a yi a shekarar 2011.

Takaitaccen tarihin Shugaba Goodluck Jonathan

Shugaba Goodluck Ebele Jonathan






An haifi Dr. Goodluck Ebele Jonathan ranar 20 ga watan Nuwambar shekarar 1957 a garin Otueke na karamar hukumar Ogbia dake a wancan lokacin yankin gabashin Najeriya, yanzu kuma yake jihar Bayelsa.


Iyayensa na sassaka jirgin kwale kwale ne.


Yayi karatun digirinsa na farko a fannin ilimin dabbobi.


Ya kuma yi digirinsa na biyu a fannin ilimin halittun ruwa.


Ya samu digirin digirgir a fannin ilimin dabbobi a jami'ar Patakwal.


Bayan da ya samu digirinsa na farko ya yi aiki a matsayin sipeton dake sa ido kan yadda malamai suke gudanar da ayyukansu, malamin jami'a da kuma jami'in dake sa ido kan kare muhalli, aikin da yake har zuwa lokacin da ya shiga siyasa.


A shekarar 1998 ne Dr. Goodluck Jonathan ya fara shiga al'amuran siyasa, inda ya shiga jam'iyyar PDP.


Ya zama mataimakin gwamnan jihar Bayelsa a shekarar 1999 bayan da Diepreye Alamieyesegha ya lashe zaben gwamnan jihar karkashin tutar jam'iyyar PDP.


Dr Goodlck Jonathan ya zamo gwamnan jihar Bayelsa bayan da majalisar dokokin jihar ta tsige Alamieyesegha bisa zargin kokarin hallata kudin haram a Burtaniya da kuma almundahana da dukiyar jama'a.


A shekara ta 2006 an zabi Dr. Goodluck Jonathan a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa, kuma bayan zaben da aka yi a shekara ta 2007 an rantsar da shi a matsayin mataimakin shugaba Umaru Musa 'Yar Adua.


Kamar ubangidansa Dr. Goodluck ya bayyana dukkan dukiyar da ya mallaka daga lokacin da ya hau kan mulki.


An rantsar da Goodluck Jonathan a matsayin mukaddashin shugaban Najeriya sakamakon rashin lafiyar da shugaban Najeriya na lokacin Umaru Musa 'Yar Adua ya yi fama da ita.


Bayan rasuwar shugaba Yar'Adua an rantsar da Goodluck Ebele Jonathan a matsayin shugaban Najeriya kuma babban kwamandan askarawan kasar.


Dr. Goodluck Jonathan na da mata daya Dame Patience Jonathan da 'ya'ya biyu.

الخميس، أبريل 14، 2011

KAMUSUN HAUSA

Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya Ta Jami'ar Bayero Ke Biya Hausawa


(Daga Bello Muhammad Danyaya)


Na jima ni kadai; ina ta tukuburi; ina cewa a raina; yaya malaman Hausa za su bar Hausawa cikin duhu game da sha'anin harshensu?


Sanin ma'anar kalmomin kowane harshe, shi ne mafi mahimmanci ga kowane dan harshen, da manazarci harshen, da ma bako mai sha'awar harshen.


Irin wannan abu ne ya sanya Turawa suka mayar da hankali da wuri, suka tattara kalmomin Hausa tare da fassara su cikin harshensu na Turanci, tare da buga abin, wanda muke kira kamus.


Tun a shekarar 1934 G.P. Bargery ya fitar da kamus dinsa mai suna Hausa-English Dictionary and English-Hausa Vocabulary (Oxford University Press, 1934).


Bayan wannan, a cikin shekarar 1962, wani Bature mai suna R.C. Abraham, ya fito da nasa kamus, wanda ya kira Dictionary of the Hausa Language (University of London, 1962).


Wadannan kamus-kamus biyu, su ne manya, kuma kansu ne aka dogara kan neman ma'anar kowace kalma ta Hausa. Duk da yake akwai wasu kamus-kamus din, wadanda ake amfani da su, amma dai wadanda aka ambata su ne manya.


Abin kulawa a nan shi ne, duk wadannan ayuka Turawa ne suka yi su.


Abin da kuma har yanzu ba a iyar da ganewa ba, shi ne, wadannan kamus-kamus da Turawa suka yi, sun yi su ne don taimakon Turanci da Turawa, da taimaka wa Bahaushe mai sha'awar Turanci.


Babu kome! Duk da haka wadannan kamus-kamus na Turawa, sun taimaka matuka, wajen adana wa Hausawa kalmomin harshensu, har zuwa yau (2007) da Allah Ya kaddari Malaman Hausa na Jami'ar Bayero suka fito da nasu kamus wanda aka yi don Hausa da Hausawa da mai sha'awar Hausa.


Tabbas, wannan kamus na Jami'ar Bayero ya zo daidai lokacin da ake matukar bukatarsa, a lokacin da wani abu wanda aka kira “Daidaitacciyar Hausa” yake neman halakar da mafi yawan kalmomin Hausa.


Daidaitacciyar Hausa, wani salo ne da ya cilasta yin amfani da karin harshen Hausa daya, tare da zabar wasu kalmomi wadanda za a yi amfani da su a rubuce-rubuce. Inda haka ke nufin wasu kalmomin ba a yarda a yi amfani da su ba. Inda haka zai yi sanadiyar barin amfani da wasu kalmomin Hausa dangurungum. A gaba kenan kalmomin harshen Hausa za su karanta, tunda wasu kalmomin an kashe su da karfi da yaji!


Alhamdu lillahi! Wannan kamus mai suna Kamusun Hausa ya tara wadannan kalmomi na Hausa, kuma daga kowane irin karin harshe na Nijeriyar Bahaushe. Kamus din ya tara tsofaffin kalmomi, da ma sababbi. Cikin tsari kamus din ya kasance, wanda zai burge kowa.


Ko ba a so, dole a ce wa mijin iya baba. Hakika duk yawan shekarun da aka diba, wajen samar da wannan kamus, da makudan kudin da aka kashe masa, da taron dangin da aka yi masa, kwalliyar da malaman suka yi masa, ta biya kudin sabulu.


A wani gefen kuma, wannan kamus ya kashe bakin tsanya; ya rusa duk wasu gunaguni masu fitowa daga irinmu, ‘yan-ga-mu-kashe-mu na Hausa!


Ina da kira! Kiran nawa shi ne, ya zama wajibi ga jami'o'i da cibiyoyi da kwalej-kwalej masu nazarin Hausa, su yi niya su mallaki wannan kamus.


Haka ma dakunan karatu, bai kamata su yi saku-saku da wannan garabasa ba.


Kai malamin Hausa da manazarci Hausa da mai sha'awar Hausa, ina ba ku shawarar, ku yi niya ku sami naku rabo. Ina yi maku gudun wannan kamus ya kare, ya zama ba a sami damar sake buga shi ba. Ku tuna Hausawa sun ce “Fara kamun safe”.


Ga mai bukatar wannan kamus mai suna Kamusun Hausa, zai iya tuntubar Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya ta Jami'ar Bayero, a ofishinta da ke harabar tsohuwar Jami'ar Bayero ta Kano. Kuma za a iya tuntubar ta, ta Jakar gidan waya. P.M.B 3011, Kano. Ko a lambar waya 060-317576, ko i-mel: csnlbuk@yahoo.com.


A cibiyar ana sayar da kwafin kamus din, a kan kudi Naira 2,000 mai makari mai kwari. Naira 1,500 mai makari mai taushi.