الثلاثاء، أبريل 19، 2011


Nuhu Ribadu

Nuhu Ribadu ya yi alkawarin kafa sabuwar Najeriya


An haifi Malam Nuhu Ribadu a ranar 21 ga watan Nuwamban 1960.


Ya samu shaidar digiri ta farko a fannin ilimin shari'a daga jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a 1983.


Ya kuma karbi shaidarsa ta zama lauya a shekara ta 1984.


Malam Nuhu Ribadu ya kara halartar jami'ar Ahmadu Bello domin karatun digiri na biyu a fannin na shari'a.


Sannan ya halarci sashin kasuwanci na jami'ar Harvard da ke Amurka.


Daga nan ne kuma ya fara aiki da Hukumar 'yan sandan Najeriya, inda ya ci gaba da aiki a matakai daban-daban, har ya zamo shugaban bangaren shari'a da gabatar da masu laifi a ofishin Hukumar da ke Abuja.


Shekaru 18 din da ya shafe yana aiki a Hukumar 'yan sandan Najeriya, ya kai har aka nada shi shugaban Hukumar yaki da yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati (EFCC) a watan Afrilun shekara ta 2003.


Yana cikin kwamitin tattalin arziki da shugaba Obasanjo ya kafa a shekara ta 2003 zuwa 2008, wanda ya haifar da sauye-sauyen da aka gudanar a bangarori daban daban na kasar.



Malam Nuhu ya bayyana aniyarsa ta tsaya wa takarar shugaban kasa a zaben da za a yi a watan Afrilu karkashin jam'iyyar adawa ta ACN a a watan Disambar 20101



Nasarar da ya samu ta hadar da cire Najeriya daga jerin kasashen da ba sa bada hadin kai ta fuskar yaki da cin hanci da rashawa.


A watan Oktoban 2007 ne kuma tsohuwar gwamnatin shugaba Umaru 'Yaradua ta cire shi daga shugabancin Hukumar ta EFCC, sannan aka tura shi ya karo karatu.


Mallam Ibrahim Shekarau



An haifi Shekarau ne a unguwar Kurmawa da ke jihar Kano, Ya kuma yi karatun Firamare a makarantar Gidan Makama daga shekarar (1961-1967).


Ya yi karantun sakandare a Kano Commercial College daga shekarar (1967-1973) sannan kuma ya garzaya jam'iyyar Ahmadu Bello da ke Zaria daga shekarar (1973-1977) inda ya samu takardar shaidar digiri ta farko.


Bayan da ya kammala karatunsa na jami'a, mallam Ibrahim Shekarau ya yi aikin gwamnati, sannan ya koma dakin karatu inda ya zama malamin lissafi a Government Technical College da ke Wudil a shekarar 1978, bayan shekaru biyu ne kuma ya zama shugaban makarantar Government Day Junior Secondary School a Wudil.


A shekarar 1980 an koma da shi makarantar Government Secondary School da ke Hadejia, sannan Government College Birnin Kudu a 1986, sai kuma Government Secondary School a Gwammaja da kuma makarantar Rumfa College a 1988, duk a matsayin shugaban makaranta.


Daga nana dai mallam Shekarau ya zama mataimakin darakta a harkar illimi a shekarar 1992, bayan kuma shekara guda aka mayar da shi darekta.


Daga nan dai likkafa ta ci gaba inda ya zama babban sakatare a ma'ikatar harkar illimi.


A watan Fabrerun shekarar 2000, malam Shekarau ya koma aikin gwamnati, kafin a koma da shi kwalejin share fagen shiga jam'ia a matsayin babban malamin lissafi.


A nan dai Shekarau ya ajiye aiki da gwamnati bayan ya yi aikin na tsawon watanni 17 a kwalejin.


Siyasa


Ba'a dauki Malam Ibrahim Shekarau a matsayin wani dan takara da zai yi tasiri ba a zaben gwamnan da aka yi a shekarar 2003 a jihar, amma daga baya kuma sai ya yi tasiri inda ya lashe zaben.


Kuma Malam shekarau ya kafa tarihi inda ya zama gwamna na farko da aka zabe shi a karo na biyu a matsayin gwamna a jihar Kano.


Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero, ya nada shi a matsayin Sardaunan Kano a karon farko a tarihin masauratar Kano.


Malam Ibrahim Shekaru ne dai dan takarar shugaban kasa, karkashin inuwar jam'iyar ANPP a Zaben watan Afrilu na shekarar 2011.

Takaitaccen tarihin janar Mohammadu Buhari

Janar Mohammadu Buhari







dansudan

An haifi Janar Muhammadu Buhari ranar 17 ga watan Disambar shekarar 1942, a garin Daura.
Tauraruwar janar Buhari ta fara haskawa a lokacin da aka bashi mukamin ministan man petur da ma'adanai a shekarar 1975, a zamanin mulkin sojin janar Olusegun Obasanjo.
Ko da yake kafin nan shi ne gwamnan sabuwar jahar Arewa maso Gabas da janar Murtala Ramat Muhammed ya kirkiro.
Daga bisani kuma aka nada shi shugaban hukumar NNPC wadda aka fara kafawa a shekarar 1977.
A zamanin mulkin Janar Sani Abacha an nada shi shugaban hukumar PTF wadda aka kafa da kudaden rarar man da kasar ta samu a wannan lokaci domin gudanar da ayyukan ci gaban al'umma.
Kuma ayyukan da janar Buhari yayi wa Najeriya kama daga hanyoyi, asibitoci zuwa makarantu yasa wasu 'yan Najeriya son ganin ya sake zama shugaban kasar.
Sau biyu janar Muhammdu Buhari yana tsayawa takarar shugaban kasar karkashin tutar jam'iyyar ANPP wato 2003 da 2007, wadanda duka bai samu nasara ba.
Rashin nasarar da ya yi karo biyu bai sauya masa ra'ayi ba game da siyasa a Najeriya, kuma tuni ya kaddamar da tashi jam'iyyar da ya kira CPC wadda yake takarar shugaban kasa a zaben da za'a yi a shekarar 2011.

Takaitaccen tarihin Shugaba Goodluck Jonathan

Shugaba Goodluck Ebele Jonathan






An haifi Dr. Goodluck Ebele Jonathan ranar 20 ga watan Nuwambar shekarar 1957 a garin Otueke na karamar hukumar Ogbia dake a wancan lokacin yankin gabashin Najeriya, yanzu kuma yake jihar Bayelsa.


Iyayensa na sassaka jirgin kwale kwale ne.


Yayi karatun digirinsa na farko a fannin ilimin dabbobi.


Ya kuma yi digirinsa na biyu a fannin ilimin halittun ruwa.


Ya samu digirin digirgir a fannin ilimin dabbobi a jami'ar Patakwal.


Bayan da ya samu digirinsa na farko ya yi aiki a matsayin sipeton dake sa ido kan yadda malamai suke gudanar da ayyukansu, malamin jami'a da kuma jami'in dake sa ido kan kare muhalli, aikin da yake har zuwa lokacin da ya shiga siyasa.


A shekarar 1998 ne Dr. Goodluck Jonathan ya fara shiga al'amuran siyasa, inda ya shiga jam'iyyar PDP.


Ya zama mataimakin gwamnan jihar Bayelsa a shekarar 1999 bayan da Diepreye Alamieyesegha ya lashe zaben gwamnan jihar karkashin tutar jam'iyyar PDP.


Dr Goodlck Jonathan ya zamo gwamnan jihar Bayelsa bayan da majalisar dokokin jihar ta tsige Alamieyesegha bisa zargin kokarin hallata kudin haram a Burtaniya da kuma almundahana da dukiyar jama'a.


A shekara ta 2006 an zabi Dr. Goodluck Jonathan a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa, kuma bayan zaben da aka yi a shekara ta 2007 an rantsar da shi a matsayin mataimakin shugaba Umaru Musa 'Yar Adua.


Kamar ubangidansa Dr. Goodluck ya bayyana dukkan dukiyar da ya mallaka daga lokacin da ya hau kan mulki.


An rantsar da Goodluck Jonathan a matsayin mukaddashin shugaban Najeriya sakamakon rashin lafiyar da shugaban Najeriya na lokacin Umaru Musa 'Yar Adua ya yi fama da ita.


Bayan rasuwar shugaba Yar'Adua an rantsar da Goodluck Ebele Jonathan a matsayin shugaban Najeriya kuma babban kwamandan askarawan kasar.


Dr. Goodluck Jonathan na da mata daya Dame Patience Jonathan da 'ya'ya biyu.

الخميس، أبريل 14، 2011

KAMUSUN HAUSA

Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya Ta Jami'ar Bayero Ke Biya Hausawa


(Daga Bello Muhammad Danyaya)


Na jima ni kadai; ina ta tukuburi; ina cewa a raina; yaya malaman Hausa za su bar Hausawa cikin duhu game da sha'anin harshensu?


Sanin ma'anar kalmomin kowane harshe, shi ne mafi mahimmanci ga kowane dan harshen, da manazarci harshen, da ma bako mai sha'awar harshen.


Irin wannan abu ne ya sanya Turawa suka mayar da hankali da wuri, suka tattara kalmomin Hausa tare da fassara su cikin harshensu na Turanci, tare da buga abin, wanda muke kira kamus.


Tun a shekarar 1934 G.P. Bargery ya fitar da kamus dinsa mai suna Hausa-English Dictionary and English-Hausa Vocabulary (Oxford University Press, 1934).


Bayan wannan, a cikin shekarar 1962, wani Bature mai suna R.C. Abraham, ya fito da nasa kamus, wanda ya kira Dictionary of the Hausa Language (University of London, 1962).


Wadannan kamus-kamus biyu, su ne manya, kuma kansu ne aka dogara kan neman ma'anar kowace kalma ta Hausa. Duk da yake akwai wasu kamus-kamus din, wadanda ake amfani da su, amma dai wadanda aka ambata su ne manya.


Abin kulawa a nan shi ne, duk wadannan ayuka Turawa ne suka yi su.


Abin da kuma har yanzu ba a iyar da ganewa ba, shi ne, wadannan kamus-kamus da Turawa suka yi, sun yi su ne don taimakon Turanci da Turawa, da taimaka wa Bahaushe mai sha'awar Turanci.


Babu kome! Duk da haka wadannan kamus-kamus na Turawa, sun taimaka matuka, wajen adana wa Hausawa kalmomin harshensu, har zuwa yau (2007) da Allah Ya kaddari Malaman Hausa na Jami'ar Bayero suka fito da nasu kamus wanda aka yi don Hausa da Hausawa da mai sha'awar Hausa.


Tabbas, wannan kamus na Jami'ar Bayero ya zo daidai lokacin da ake matukar bukatarsa, a lokacin da wani abu wanda aka kira “Daidaitacciyar Hausa” yake neman halakar da mafi yawan kalmomin Hausa.


Daidaitacciyar Hausa, wani salo ne da ya cilasta yin amfani da karin harshen Hausa daya, tare da zabar wasu kalmomi wadanda za a yi amfani da su a rubuce-rubuce. Inda haka ke nufin wasu kalmomin ba a yarda a yi amfani da su ba. Inda haka zai yi sanadiyar barin amfani da wasu kalmomin Hausa dangurungum. A gaba kenan kalmomin harshen Hausa za su karanta, tunda wasu kalmomin an kashe su da karfi da yaji!


Alhamdu lillahi! Wannan kamus mai suna Kamusun Hausa ya tara wadannan kalmomi na Hausa, kuma daga kowane irin karin harshe na Nijeriyar Bahaushe. Kamus din ya tara tsofaffin kalmomi, da ma sababbi. Cikin tsari kamus din ya kasance, wanda zai burge kowa.


Ko ba a so, dole a ce wa mijin iya baba. Hakika duk yawan shekarun da aka diba, wajen samar da wannan kamus, da makudan kudin da aka kashe masa, da taron dangin da aka yi masa, kwalliyar da malaman suka yi masa, ta biya kudin sabulu.


A wani gefen kuma, wannan kamus ya kashe bakin tsanya; ya rusa duk wasu gunaguni masu fitowa daga irinmu, ‘yan-ga-mu-kashe-mu na Hausa!


Ina da kira! Kiran nawa shi ne, ya zama wajibi ga jami'o'i da cibiyoyi da kwalej-kwalej masu nazarin Hausa, su yi niya su mallaki wannan kamus.


Haka ma dakunan karatu, bai kamata su yi saku-saku da wannan garabasa ba.


Kai malamin Hausa da manazarci Hausa da mai sha'awar Hausa, ina ba ku shawarar, ku yi niya ku sami naku rabo. Ina yi maku gudun wannan kamus ya kare, ya zama ba a sami damar sake buga shi ba. Ku tuna Hausawa sun ce “Fara kamun safe”.


Ga mai bukatar wannan kamus mai suna Kamusun Hausa, zai iya tuntubar Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya ta Jami'ar Bayero, a ofishinta da ke harabar tsohuwar Jami'ar Bayero ta Kano. Kuma za a iya tuntubar ta, ta Jakar gidan waya. P.M.B 3011, Kano. Ko a lambar waya 060-317576, ko i-mel: csnlbuk@yahoo.com.


A cibiyar ana sayar da kwafin kamus din, a kan kudi Naira 2,000 mai makari mai kwari. Naira 1,500 mai makari mai taushi.

الجمعة، فبراير 11، 2011

Shugaba Mubarak na Misra ya yi Murabus, Jama'a na ta Murna

Shugaba Hosni Mubarak na Misra ya yi murabus bayan zanga-zangar kwanaki 18 da Masarawa su ka yi, na neman kawo karshen shugabancinsa na tsawon shekaru 30.

Masu zanga-zangar kin gwamnati ke nan ke murna a Dandalin Tahrir saboda murabus din da Shugaba Hosni Mubarak ya yi.
Mai Hoto: ASSOCIATED PRESS

Masu zanga-zangar kin gwamnati ke nan ke murna a Dandalin Tahrir saboda murabus din da Shugaba Hosni Mubarak ya yi.

Shugaba Hosni Mubarak na Misra ya yi murabus bayan zanga-zangar kwanaki 18 da Masarawa su ka yi, na neman kawo karshen shugabancinsa na tsawon shekaru 30.

Dubun dubatan Masarawa ne su ka bazu zuwa kan tituna cikin murna da farin ciki don yin bikin wannan sanarwar ta yau Jumma’a da Mataimakin Shugaban Kasa Omar Suleiman ya yi, wanda y ace an mika ikon na shugaban kasa ga hukumar soji. Gidan Talabijin na kasar y ace za a bayar da cikakken bayani an jima kadan a yau dinnan jumma’a kan yadda sojojin za su shugabanci kasar.

Dandalin Tahrir da ke birnin al-Khahira --- wanda nan ne ma bijirewar ta fi kamari --- ya barke da sowar shagulgula.

Dubban wadanda su ka yi zanga-zangar sun yi ta ihu cike da murna har bayan sa’a guda da jin sanarwar ta murabus din Mubarak. Mutane da dama sun yi ta daga tutucin Misra a sailinda wutar nuna alamar farin ciki k eta haskaka sararin subahana. Wasu dinbin mutanen kuma sun yi ta shagulgula a kan titunan birnin Askandariyya, inda motoci da dama su ka yi ta busa. A sauran biranen ma an yi ta shagulgula.Wannan ‘yar takaitacciyar sanarwar ta Suleiman ta zo ne bayan sama da makonni biyu na zanga-zangar kin gwamnati. Mataimakin shugaban kasar ya ce Mr. Mubarak ya yi la’akari ne da ‘mawuyacin halin da kasar ta fada ciki.’

Wasu kafafen yada labarai sun ruwaito jami’an gwamnati na cewa Mr. Mubarak ya bar babban birnin kasar zuwa gidansa da ke mashakatar Sham El-Sheikh da ke kusa da gabar Bahar Maliya.

A halin da ake ciki kuma, dab da kammala rubuta wannan labarin, Shugaban Amurka Barack Obama, ya kammala jawabinsa kan murabus din da Mubarak ya yi, inda ya yi na'am da al'amarin ya kuma ce Amurka za ta cigaba da hada hannu da gwamnatin Misra.

Kafin nan dai Mataimakin Shugaban Amurka Joe Biden, ya ce murabus din shugaban Misra Hosni Mubarak ya bude wani sabon babi a tarihi.

Ya yi wannan maganar ce a jihar Kentucky ta Amurka, gabanin jawabin Shugaba Barak Obama a birnin Washington.

Biden y ace tun farkon wannan zanga-zangar Amurka ta dage kan cewa Masarawa ne za su zabi makomar Kasarsu.

Y ace Amurka ta tsaya kan muhimman manufofinta lokacin da ake zanga-zangar --- ciki har nuna cewa duk wani yinkurin musguna wa masu zanga-zangar baa bin amincewa ba ne, da kuma kiraye-kirayen a mutunta ‘yancin Masarawa tare da biya masu bukata. Y ace Amurka ta kuma bukaci shirin gyare-gyare a siyasar Misra ya zama mai dorewa a kuma fara tattauna hanyar komawa ga tafarkin dimokaradiyya.

‘Yan Majalisan Tarayyar Amurka sun yaba da murabus din da Mubarak ya yi. Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa Harry Reid y ace ya yi farin ciki da yadda Mubarak ya ‘saurari mutanen Misra.’ Dan Majalisar Dattawa dan Republican John McCain ya yaba da matakin da Mubarak ya dauka. McCain, wanda shi ne dan takarar shugaban kasar jam’iyyarsa a zaben 2008, y ace tarihi zai nuna cewa matakin da shugaban na Misra ya dauka na baya bayannan shi ya fiye wa kasarsa.

Amurka na bai wa Misra taimako ta fuskar soji da ya kai sama da dala miliyan dubu dari da uku a kowace shekara. Wasu ‘yan Majalisar Dokokin Amurka sun bukaci a daina bayar da wannan taimakon muddin aka yi jinkirin gyare-gyare a gwamnatance a kasar

مبارك يتنحى والجيش يدير البلاد

قال عمر سليمان نائب الرئيس المصري -في بيان مقتضب عبر التلفزيون المصري- إن الرئيس حسني مبارك قرر التخلي عن "منصب رئيس الجمهورية وكلف المجلس الأعلى للقوات المسلحة بإدارة شؤون البلاد".

ووفقا لسليمان فإن هذه الاستقالة جاءت "في هذه الظروف العصيبة التي تمر بها البلاد".

وفور إعلان سليمان قرار مبارك تنحيه عن السلطة لوح ملايين الثوار المصريين بالأعلام وغنوا "الشعب أسقط النظام" وبكوا وهتفوا وعانق بعضهم البعض في هذه اللحظة التاريخية من تاريخ مصر والعالم العربي.

الرئيس المخلوع غادر القاهرة لوجهة مجهولة (الفرنسية-أرشيف)
تطوير الأساليب
وتأتي استقالة مبارك بعد تظاهرات عارمة قدرت بالملايين جابت شوارع مصر وميادينها العامة يوم الجمعة، في حين طور الثوار أساليبهم بمحاصرة مؤسسات حيوية كبرى ومن ضمنها قصر العروبة الرئاسي بمصر الجديدة والتلفزيون الحكومي وقصر رأس التين بالإسكندرية.

وكان الثوار قد أحكموا قبضتهم منذ يومين على رئاسة الوزراء ومجلسي الشعب والشورى.

كما جاءت الاستقالة بعد وقت قصير من الإعلان عن أن الرئيس المخلوع وأفراد أسرته غادروا القاهرة إلى وجهة مجهولة رجحت جهات كونها شرم الشيخ.

وكانت حالة غضب شديد قد سيطرت على المعتصمين بميدان التحرير البارحة وفي مختلف أنحاء مصر بعد سماعهم خطاب مبارك الذي أعلن تفويضه عمر سليمان صلاحياته الرئاسية، وإلغاء حالة الطوارئ "عندما تسمح الظروف الأمنية"، دون أن يقدم استقالته من منصبه كما توقع المصريون يوم أمس.

محمد حسين طانطاوي يرأس المجلس الأعلى للقوات المسلحة (رويترز)
مطالب مشروعة
كما رفضوا بشدة بيانا لعمر سليمان -جاء بعد خطاب مبارك بوقت قليل- ودعا فيه الثوار إلى العودة إلى "ديارهم".

وكان المجلس الأعلى للقوات المسلحة قد أصدر أمس بيانه رقم واحد الذي أشار فيه إلى التزامه بالدفاع عن مطالب الشعب المشروعة وبقاء المجلس الأعلى للقوات المسلحة في حال انعقاد.

وصدر صباح الجمعة بيان ثان للمجلس الأعلى قال فيه إنه سيضمن الانتقال إلى الديمقراطية بما فيها تنظيم انتخابات رئاسية "حرة"، ورفع حالة الطوارئ بمجرد أن تسمح الظروف الحالية وضمان إجراء انتخابات رئاسية وصفها بالحرة.

وتعهد الجيش بـ"ضمان" إصلاحات تعهد بها مبارك والفصل في الطعون الانتخابية وإجراء التعديلات التشريعية اللازمة.

فرحة عارمة عمت مصر والعالم العربي برحيل مبارك (رويترز)
تطورات متلاحقة
وعزا إصدار هذا البيان إلى "التطورات المتلاحقة للأحداث الجارية والتي يتحدد فيها مصير البلاد وفي إطار المتابعة المستمرة للأحداث الداخلية والخارجية وما تقرر من تفويض لنائب الرئيس من اختصاصات".

وأكد الجيش في البيان أنه سيلتزم برعاية مطالب الشعب والسعي لتحقيقها من خلال تنفيذ الإجراءات في التوقيتات المحددة لضمان انتقال سلمي للسلطة.

ونزل الجيش لأول مرة إلى الشوارع يوم 28 يناير/ كانون الثاني 2011 بعد اندحار قوات الشرطة والأمن المركزي أمام الثوار المطالبين بتنحية الرئيس المخلوع.

وتأتي هذه التطورات المتلاحقة في وقت أعلن فيه اليوم الأمين العام للحزب الوطني الديمقراطي الذي كان يحكم مصر، حسام بدراوى، استقالته من منصبه بعد أقل من أسبوع من تعيينه.

وأبلغ بدراوي قناة الحياة التلفزيونية بأنه قدم استقالته احتجاجا على الطريقة التي أدار بها النظام ما أسماه الأزمة السياسية الأخيرة.

الخميس، فبراير 10، 2011

مبارك يفوض نائبه سلطات الرئيس

مبارك على عكس المتوقع لم يعلن في خطابه للشعب تنحيه (رويترز)

أعلن الرئيس المصري حسنى مبارك في خطاب للشعب مساء الخميس أنه فوض نائبه عمر سليمان اختصاصات رئيس الجمهورية وفق ما يحدده الدستور. وقد لاقي هذا الخطاب رفضا مباشرا من المحتشدين في ميدان التحرير الذين رددوا بصوت واحد "إرحل".
وكانت أبناء تواترت عن ترجيح أن يُعلن مبارك الليلة رسميا تنحيه وأن تنتقل السلطة إلى القوات المسلحة التي عقد قادتها اليوم اجتماعا مفتوحا في غياب مبارك, وسط أنباء عن رفض قادة الجيش نقل السلطة لعمر سليمان نائب الرئيس.
وجاء هذا التطور على أثر اجتماع مفتوح للمجلس الأعلى للقوات المسلحة برئاسة وزير الدفاع المشير محمد حسين طنطاوي, ووسط ثورة شعبية عارمة بدأت في 25 يناير/كانون الثاني الماضي.
وقد ذكرت شبكة إن بي سي الأميركية نقلا عن مصدرين مصريين وصفتهما بالمستقلين أن مبارك (82 عاما) سيتنحى الليلة, وهو ما رجحه لاحقا مدير وكالة المخابرات المركزية الأميركية (سي آي أيه).
وقالت مصادر للجزيرة إن الجيش أصدر البيان رقم واحد بعد تحفظه على خطاب كان مبارك يعتزم إلقاءه, ويعلن فيه نقل صلاحياته إلى نائبه عمر سليمان. وأعلن التلفويون المصري لاحقا عن خطاب يتوجه به مبارك الليلة للمصريين.
وقبل هذا, كانت القوات المسلحة المصرية قد أصدرت البيان رقم واحد الذي قال إن المجلس الأعلى للقوات المسلحة قرر الانعقاد بشكل دائم لمتابعة الأوضاع في مصر.
وجاء في البيان أن المجلس عقد اجتماعه برئاسة القائد العام للقوات المسلحة ووزير الدفاع محمد حسين طنطاوي "انطلاقا من مسؤولية القوات المسلحة والتزاما بحماية الشعب ورعاية مصالحه وأمنه وحرصا على سلامة الوطن والمواطنين ومكتسبات شعب مصر العظيم وممتلكاته, وتأكيدا وتأييدا لمطالب الشعب المشروعة انعقد اليوم الخميس الموافق العاشر من فبراير 2011 المجلس الأعلى للقوات المسلحة لبحث تطورات الموقف حتى تاريخه, وقرر المجلس الاستمرار فى الانعقاد بشكل متواصل لبحث ما يمكن اتخاذه من إجراءات وتدابير للحفاظ على الوطن ومكتسبات وطموحات شعب مصر العظيم".
وقبل دقائق من صدور البيان الأول للقوات المسلحة, كان ضابط كبير في الجيش قد أبلغ مئات آلاف المتظاهرين في ميدان التحرير أن كل مطالبهم ستتحقق.
وقد أثار ذلك حالة من الابتهاج في صفوف المتظاهرين الذين تجاوز عددهم المليون, والذين حاصروا في وقت سابق مقر الحكومة مما اضطر رئيس الوزراء إلى نقل اجتماعات الوزراء إلى مقر وزارة الطيران المدني, كما حاصروا مجلسي الشورى والشعب.
وسبق أيضا البيان رقم واحد للقوات المسلحة تصريحات لرئيس الوزراء أحمد شفيق وأمين عام الحزب الوطني الحاكم حسام بدوراي أشارا فيها إلى أن مبارك سيتنحى عن السلطة التي أمضى فيها نحو 30 عاما.
وبينما كانت الأنباء تتضارب مساء الخميس بشأن ما إذا كان مبارك يتأهب بالفعل للتنحي, قال شفيق إنه لا يزال ممسكا بالسلطة. لكن مسؤولين آخرين أشاروا بوضوح إلى مفاوضات جارية لنقل السلطة.
بيد أن وزير الإعلام أنس الفقي تحدث في الوقت نفسه عن مجرد "شائعات" ترددها وسائل الإعلام.
يذكر أن مصر تشهد منذ 25 يناير/كانون الثاني الماضي ثورة شعبية تطالب الرئيس مبارك ورموز نظامه بالرحيل.
وكان مقررا تنظيم مظاهرات حاشدة جديدة يوم غد الجمعة لحمل مبارك على الرحيل.

ترقب بميدان التحرير لبيان مبارك

مئات الآلاف احتشدوا بميدان التحرير انتظارا لما وصفوها باللحظة التاريخية (الأوروبية)
توافد آلاف من المصريين مساء اليوم إلى ميدان التحرير عقب سماعهم البيان الصادر عن القوات المسلحة المصرية بتأييدها لمطالب المحتجين في الميدان.
وقال مشاركون في الاحتجاجات إن الآلاف بدؤوا مسيرات من مختلف مناطق القاهرة للانضمام إلى المتظاهرين الذين وصل عددهم نحو ثلاثة ملايين في الميدان والساحات المحيطة به ترقبا للتطورات الحاسمة التي يتوقع أن تحدث خلال وقت قصير، خاصة بعد إعلان التلفزيون المصري عن بيان للرئيس الساعة العاشرة بتوقيت القاهرة (الثامنة بتوقيت غرينتش).

وردد آلاف من الموجودين في الميدان شعارات تصر على تنحي مبارك، كما هتفوا "الجيش والشعب يد واحدة".
وسلم ضابط برتبة رائد سلاحه وانضم إلى المتظاهرين، وقال أحمد علي شومان للجزيرة من وسط الجموع المحتشدة إن الدور يجب أن يكون للجيش لإنهاء الحالة التي تمر بها مصر.
وأكد أن النظام سقطت شرعيته وناشد قادة الجيش القيام بدورهم، وقال إن مهمة الجيش هي حماية الشعب وليس حماية النظام.
وكان التلفزيون المصري قد أذاع في وقت سابق بيانا باسم الجيش المصري قال فيه إنه سيلتزم بمطالب الشعب المصري.
جمعة التحدي
وكان المتظاهرون يستعدون أصلا للخروج في مظاهرات حاشدة يوم غد الذي أطلق عليه جمعة التحدي أو الزحف، في حين دخلت الثورة المصرية يومها الـ17 وسط انضمام قطاعات عمالية ومهنية عديدة إلى عمليات الاحتجاج.
وأعلن ائتلاف الثورة أن المظاهرات ستنطلق غدا من عدة مساجد بالقاهرة للمطالبة بتنحي مبارك عن السلطة. وسرت شائعات عن نية المعتصمين في ميدان التحرير محاصرة عدد من المواقع المهمة.

واستباقا لتلك الخطوة -في ما يبدو- انتشر الجيش قرب عدد من المواقع الحيوية مثل القصر الرئاسي ومبنى الإذاعة والتلفزيون على كورنيش النيل، فضلا عن مباني عدة وزارات قرب ميدان التحرير وسط العاصمة المصرية.

ورغم تساقط الأمطار الغزيرة على ميدان التحرير اليوم، واصل آلاف المحتجين تدفقهم على الميدان لإرغام الرئيس مبارك -الذي يحكم البلاد وسط حالة طوارئ منذ بداية ثمانينيات القرن الماضي- على ترك سدة الرئاسة.

مظاهرات عمال قناة السويس (الجزيرة)
محامون وأطباء
وعند مدخل الميدان من جهة شارع طلعت حرب، انضم آلاف المحامين إلى عشرات الآلاف من المحتجين المحتشدين منذ أمس، وهم يرددون "الشعب يريد إسقاط النظام" وعشرات الشعارات الأخرى. وقبيل ذلك مر المحامون بباحات قصر عابدين الرئاسي وهم يرددون شعارات تدعو الرئيس مبارك للرحيل.
وعند مدخل الميدان الغربي، احتشد الآلاف من الأطباء الذين جاؤوا من مستشفى القصر العيني للانضمام إلى المتظاهرين في الميدان.
اعتصام مفتوح
من جهة أخرى بدأ نحو خمسة آلاف من سائقي وعمال هيئة النقل العام في القاهرة اعتصاما مفتوحا للمطالبة بتحسين الأجور ورفع حوافزهم.
وفي أسيوط بصعيد مصر، استمرت الاعتصامات والاحتجاجات التي تشمل الجامعة وشركات الأدوية والغاز والكهرباء.
وقد انتقل عدوى المظاهرات إلى مطار القاهرة الدولي الذي شهد اليوم مظاهرات عديدة مطالبة بتحسين أوضاع العاملين وتثبيت العمالة المؤقتة.
كما تظاهر ألفان من موظفي مدينة الإنتاج الإعلامي مطالبين بإقالة وزير الإعلام وإسقاط مبارك.
كما توقفت الحركة السياحية في مدينة الأقصر المصرية، وخلت المناطق الأثرية والسياحية في المدينة تقريبا من السياح.
وتظاهر آلاف العمال في السويس وبورسعيد وكفر الشيخ والغربية وأسيوط وسوهاج، مطالبين برفع ما وصفوه بالظلم عنهم وتنحي الرئيس المصري






Sojojin Masar Sun Ce Sun Tsoma Hannu Don Ceto Kasar

Sojoji da jami'an jam'iyya mai mulki sun ce shugaba Hosni Mubarak zai biya bukatun masu zanga-zangar neman saukarsa, kuma zai yi jawabi in an jima


Masu zanga-zanga a dandalin Tahrir a birnin al-Qahira


Gidan telebijin na Masar yace nan da jimawa a cikin daren alhamis din nan shugaba Hosni Mubarak zai yi jawabi ga al'ummar kasar. Tun da farko a yau din, hafsoshin sojan kasar da kuma jami'an jam'iyya mai mulki sun ce shugaban "zai biya bukatun" masu zanga-zangar neman saukarsa daga kan mulki.

Misrawa sun yi kwanaki 17 su na zanga-zangar neman hambarar da shugaba Mubarak, wanda yayi shekaru kusan talatin yana mulkin kasar. Sun bukaci da ya sauka ba tare da wani jinkiri ba.

A yau alhamis, majalisar koli ta soja ta yi wani taro ba tare da shi shugaba Hosni Mubarak ba, wanda shi ne babban kwamandan sojojin kasar.

Rundunar sojojin ta fito a telebijin tana bayyana cewa tana goyon bayan "halaltattun bukatun jama'ar kasar." Wani kakakin majalisar koli ta sojan yace majalisar tana nazarin matakan da zata iya dauka domin kare kasar da al'ummarta.

An barke da sowa ta murna a fadin dandalin Tahrir, cibiyar wannan zanga-zanga, a lokacin da wannan labari ya bazu daidai faduwar rana agogon kasar.

الثلاثاء، فبراير 01، 2011

Rundunar Mayakan Masar Tayi Alkawarin Ba Zata Yi Amfani Da Karfi Kan Masu Zanga Zanga Ba

Rundunar sojojin Masar ta fada jiya litinin cewa ta yarda da hakkinda ‘yan kasar suke das hi na
dagewa kan bukatunsu,daga nan ta lashi takobin ba zata yi amfani da karfikan jama’a ba.


Rundunar sojojin Masar ta fada jiya litinin cewa ta yarda da hakkinda ‘yan kasar suke das hi na dagewa kan bukatunsu,daga nan ta lashi takobin ba zata yi amfani da karfikan jama’a ba.


Sanarwar rundunar sojin tazo ne yayinda dubun dubatan ‘yan kasar Masar din suke ci gaba da zanga zanga a dandalin tahrir,suna ci gaba dab iris da dokar hana yawon dare a a dare na hudu,suna ci gaba da lallai lallai sai a kawo karshen mulkin shugaba Hosni Mubarak na tsawon shekaru 30.


Daga bisani sabon mataimakin shugaban kasar da aka nada ya fito a tashar talabijin ta kasar yace shugaba Hosni Mubarak ya umurce shi da ya fara tattaunawa da dukkan kungiyoyin siyasa da nufin kaddamar da sauye sauyen siyasa a kasar. Mataimakin shugaban kasa Omar Suleiman bai fayyace abinda sauye sauyen zai kunsa ba,da kuma wadanne kungiyoyi ne zai tuntuba.


Masu zanga zanga sun ayyana wata gagarumar zanga zanga a yau Talata inda mutane milyan daya zasu fita kan titunan Alkahira.


Sanarwar da rundunar sojojin kasar ta bayar bata fayyace ko ta dauki bukatar da mutane suke yi na shugaba Hosni Mubarak ya yi murabus a halattacciya ba,ko dai buktar sauye sauye ne suke kallo a matsayin halattacce.


Kafofin yada labarai a Masar sun bada labarin Mr. Mubarak ya nada sabon minsitan harkokin cikin gida da kuma na kudi,a wani mataki na shawokan masu zanga zanga.Ministan harkokin waje da na tsaro garambawul da aka yi bai taba su ba.


Dubban ‘yan kasashen ketare dake kasar ne suka yi ta tururuwan barin MAsar jiya litinin. Amurka ta bada labarin ta kwashe ‘yan kasarta 1,200 da jiragen sama tara da gwamnati tayi shatarsu zuwa Turkiyya,Cyprus,da Girka a cikin sa’o’I 24 da suka wuce. Haka kuma tace tana sa ran jigilar wasu 1,400 cikin kwanaki masu zuwa