الأحد، يناير 17، 2010

Kissar Annabi Adam (As) Na Uku

To dayake an hallici Hauwa'u daga bangaren jikin Annabi Adam as ne don sai All.. madaukakin sarki ya sanyata ta zama matar sa don haka ne ma bayan da aka halicce ta sai ya kale ta lokacin daya ganta sai yaga tayi kama dashi sosai amma sai yaga tafishi rauni na yanayin jiki, wannan yasa ya tambaye ta ke wacece kuma? Sai ta bashi amsa da cewa nice hauuwa ni abin halittar ubanjigi ne

sai yaga lallai hauwwa'u tana magana ne irin nashi kuma da ya sake lura sai yaga tayi kama dashi sosai kuma yaji a cikin zuciyar sa lallai ya kamu da kaunar ta to daga nan fa sai ya gana da ubagijin sa yace ya ubangiji wannan wacce irin halitta ce kyakyawa a kusa dani hakika nayi farin ciki sosai da ganin ta, sai kawai yaji magana daga ubangiji yana cewa wannan itace abin halittar mu Hawwa shin kana son ta? Domin ka samu nastauwa da ita nan take sai Annabi Adam As yace kwarai da gaske, kuma ina godiya ga All.. da wannan ni'ima da yayi mini daga cikin tsatsona , daga nan sai All.. madaukakin sarki ya umaci Annabi Adam As daya nemi auren hauwa, sai Annabi Adam As yabi Umarnin da akayi bashi kuma aka sanya koyar da Addini gareta ya zama shine sadakin ta wannan yada All.. ya amince da wannan tunda ya bi umarnin da aka bashi sai ya bukaci hauwa ta biyo shi sai taki amincewa sai ta bukaci ya biyo ta saiya bita, daga nan dai aka fara rayuwar zamantakewa tsakanin Annabi Adam da Hauwa'u haka dai suka ci gaba da rayuwar taimakekeniya tsakanin su har dai ta hanyar ilhama mala'ika jibrilu ya nuna musu hanyar da zasubi suyi noma, suka ci gaba da noma alkama da dai sauran su kuma suka koyar da ya'yan su yadda zasuyi zamantakewa da juna da kuma yadda maza da mata zasu taimakawa juna a cikin alumma,

to yanzu kuma zamu kawo muku yadda auren yayan Annabi Adam suka haifa ya kasance , to kamar yadda yazo acikin tarihi tun bayan da aka saukar da Annabi Adam da Hauwa'u a gidan duniya suka daukar ma kansu tattara iyalansu wuri guda yadda zasu wastu a fadin duniya baki daya, don haka bada jimawaba sai kawai ummuna Hauwa'u ta dauki ciki kuma ta haifi yayaye 2 tagwaye na miji da mace aka sanya sunan da namijin kabila sunan mace din ikilima bayan da aka dauki dogon lokaci kuma sai ta kara daukar wani cikin kuma ta haifi ‘yan biyu a wannan karon ma na miji da mace sai aka sanyawa na mijin suna Habila ita kuma ta mace din aka sanya mata suna layuza, to sai dai All. yayiwa Layuza kyakyawan kira mai kyau wato kyakyawace kuma itace wadda tafi kyau acikin yayan Annabi Adam (As) wanda hakan yasa Annabi Adam a kowanne lokaci yana ji mata tsoron hastari ko wani abu ya faru da ita , lokacin da dukkan wadan nan yaran suka girma suka zama samari suka kai lokacin balaga

kuma suka kai munzinin Aure sai All.. madaukakin sarki ya yi wahayi ga Annabi Adam da ya Aurar da layuza yar shi kyakyawa da ga danshi Habila ita kuma ikilima a aurar da ita ga Kabila , nan take sai Annabi Adam ya sanar da umarnin Ubangiji ga yayan sa amma sai wani daga cikin yayan sa ya nuna rashin amincewa da wannan umarni wato kabila ken an yace yaya za'a aurar da yar uwata mai kyau ga habila ni kuma a dauki yar uwar shi layuza mummuna a aurara da ita gare ni, daga nan sai hasada da kawadiyi suka motsa ya kai kabila yana tuhumar mahaifinsa yana magana da zafin rai cewa lallai All.. bai bada irin wannan umarnin ba kai ne dai ka kitsa ma kanka abinda kakeso, amma sabon da Annabi Adam as ya tabbatarwa da ‘ya'yansa gaskiyarsa kuma cewa abinda yake fadi gaskiya ne ba da kashin kanshi bane yayi haka, ubangiji ne ya bashi umarnin haka, don haka sai yacewa yayan sa kowanne su yayi layya ga All.. madaukakin sarki duk wanda aka amsa layyanshi to shine mai gaskiya kuma alamar da zata bayyana da zai gane wanda aka karbi layyansa shine tsawa daga sama zata fado daga sama ta kona shi, sai dukkan yayan sa suka amince da wannan zabi , sai Habila ya samu akuya mai kiba da aka kiwata , kuma akuyar da tafi kiba da cika acikin akuyoyin da yake dashi, amma shi kabila da yake shi ba makiyayi bane manomi ne sai ya dauki wani dami karami amastayin abinda zaiyi layya dashi, kowaya yah au saman dutse da abin layyansa kowanne su ya kaddamar da layyansa ba tare da bata wani dogon lokaci ba sai ga tsawa ta sauko daga sama ta kona akuyar nan amma tabar damin nan agefe, wanda haka ya tabbatar da cewa an amshi layyan habila ke nan kuma shine mai gaskiya, kuma ya bayyana afili cewa lalai habila shine mai biyayya ka ubangijin sa shi kuwa kabila yana daga cikin masu nuna taurin kai ga umarnin ubangiji, to sai dai akwai wata ruwayar ma game da batun yayan Annabi Adam da hauwa'u amma wadda muka ambata ita tfi shahara tsakanin malaman tarihi,
to daga nan kuma sai lamarin ya dauki wani sabon salo inda kabila ya fara nuna Hasada na meyasa All. bai Amshi layyanshi ba, yasa fuskarshi ta canza saboda bakin ciki da bacin rai, har yakai ya fadama habila cewa zai kashe shi, amma da yake habila mutum ne mai tsarkin zuciya kuma yana da karfin Imani sai yayi masa Nasiha yace masa All.. yana Amsar aikin da akayi shi ne da niyya mai kyau kuma da ikhlasi,don haka yana da kyau ka kasance mai ikhlasi kafin All. ya amsa ayyukan ka, Idan kanaso ka kasheni to ni bani da niyar daukar irin wannan mataki akan ka,domin ni ina tsoron ubangijin wannan duniyar da abinda ke cikinta. to sai dai nasiyar habila ba tayi wani tasiri ba ko kadan a cikin zuciyar kabila don kuwa zuciyarsa sat a riga ta sawwala masa daukar matakin kashe dan uwansa,
A cikin irin wannan yanayin ne shedan yayi amfani da damar da ya samu ya dinga sanya waswasi a cikin zuciyar kabila yana ce masa an karbi layyyar da dan uwanka habila yayi amma kai ba'a amshi naka ba, idan har ka bar habila a raye to zai haifi ‘ya'ya wanda a nan gaba zasu rika gorantawa ‘ya'yan ka suna alfahari da cewa an amshi layyar mahaifin su amma ba'a amshi layyar ka ba, haka dai shedan yayi ta nanata masa irin wannan zuga da sanya waswasi har dai ya samu wata dama lokacin Annabi Adam (As) zai kai ziyara zuwa dakin ka'aba dakin All.. a makka don haka lokacin da kabila yaga mahaifinsu baya nan sai ya zo inda habila yake ya fara gaya masa bakaken maganganu domin ya fusata shi, yace wato an amshi layyarka amma ba'a amshi nawaba ko? Yanzu kanaso in gamasu kuma in amince da Aurar da yar uwata kyakyawa da akayi gareka, kuma a bani yar uwarka mummuna ba zan taba yarda ba har abada, sai habila ya bashi amsa da cewa ya dauke hannun ka daga zalunci da hassada da kake nuna min daga karshe dai sabani da jayayya tayi kamari tsakaninsu wato habila da kabila har dai ya kai kabila ya fara tunanin yaya zai yi ya kashe dan uwan sa habila nan take sai shedan ya fara sawwara masa yanayi masa waswasin cewa ka sanya kanshi a tsakiyar dutse sai ka hada duwastun nan da da nan zakaga ya mutu sai kabila yayi amfani da wannan dabarar da shedan ya kitsa masa ya kashe dan uwan sa yayi shahada bisa zalunci.
To sai dai bayan da ya kashe dan uwansa sai ya rude ya rasa yadda zai yi ya suturta gawansa wato ya bizne shi kenan don haka yayi ta yawo da gawan dan uwansa a wuya yana cikin takaici da nadama, har dai yadda wasu angulu guda biyu sukazo suna fada da junan su har dai daya ta kashe daya sai ta sanya kumbarta ta haka rami sai ta jefa gawar yar uwarta a ciki, anan ne fa kabila ya kara tabbatar da raunin sa inda ya kai da kansa yana cewa ya kaiton shi yanzu sai da Angulu ta nuna min yadda zan bizne gawar dan uwana hakika ina cikin bata bayyanan na, bayan da ya kammala bizne dan uwansa sai ya kama hanya ya koma gida lokacin da Annabi Adam yaga kabila shi kadai ba ta re da dan uwansa habila ba da suka fita tare sai ya tambayeshi ina danuwanka yake, sai ya fara kame - kame yana kaucewa har dai ya kai ga ya dauki mahaifinsa ya nuna masa kabarin dan uwansa da yake nufin lallai ya kashe shi, wannan lamarin ya tayar da hankalin Annabi Adam as matuka ya dauki jana izar dansa to sai dai da yake lokacin da jinin dansa ya zuba a kasa, kasa ta shanye don haka sai ya la'anci wannan wurin wanda hakan yasa tun daga wancan lokaci idan jinin mutum ya zuba, kasa bata shanye jininsa, kamar yadda yazo a cikin tarihi All..hu A'alam

daga nan kuma sai Annabi Adam As ya yi zaman makoki na kwanaki 40 saboda bakin cikin rabuwa da dansa, sai dai dama lokacin da aka kashe habila matarsa ta kasance tana da ciki don haka bayan da ta haihu sai ya bata kyauta domin girmamawa ga mahifin dan kuma mijinta habila, bayan nan kuma sai All. madaukakin sarki ya bawa Annabi Adam da Mai sauna Shi's wa to Hibbatullah , wanda lokacin da ya girma ya kai munzinin Aure sai aka aurar Masa mace mai suna Na'ima haka dai zuri'arar sa ta ci gaba da yaduwa daga tsatson habila , wannan dai shine yadda rayuwarsa ta ci gaba da kasancewa har zuwa lokacin da shekarunsa suka tura girma ya kamashi, kuma yana dan shekaru Dari tara da talatin ya amsa kiran All.. ya bar gidan duniya ya bar gadon Annabci ga dansa Shi'ts wanda lokacin da Mahaifinsa Annabi Adam as ya kwanta rashin lafiya wadda daga ita bai sake tashi ba kuma ya kasance shine yake jiyyarta don haka nema lokacin da ya koma ga All.. sai ya yi masa wanka kuma ya Bizne shi a birnin Makka Aminci All.. ya tabbata gareshi lsanda aka haifeshi da sanda ya koma ga ubangijinsa, don haka shai'ts ya tsaya makwafin mahaifin shi ya ci gaba da koyar da Al'umma Ilimi kamar yadda mahaifinsa yayi masa wasiya.

ليست هناك تعليقات: