السبت، فبراير 25، 2012

عرض متحف سودانيين الهوسا View sudanese Hausa Museum


الطب البلدي لابناء الهوسا ( التداوي بالاعشاب )

طلاب و طالبات الهوسا في جامعة البحر الاحمر

طالب من اتحاد طلاب الهوسا في جامعة البحر الاحمر يرتدي لبسة هوساوية

بتات الهوسا في كسلا في مهرجان ثقافي يعرضن تراث الهوسا

طالب من اتحاد طلاب الهوسا في جامعة البحر الاحمر يقدم برنامج في الحفل الختامي للمحرجان


طالب من اتحاد طلاب الهوسا في جامعة البحر الاحمر يرتدي ملابس هوساوية يشرح للزوار الكرام


ادوات التى تستخدم في المنازل قبل التكنلوجية و الادوات هم راغية و هي مثل الثلاجة , غورية

عرض اتحاد طلاب الهوسا في مهرجان جامعة البحر الاحمر ماكولات الهوسا ( قدو قدو / فوره , عصيدة / تُوو , قورو , كلوه , دداوه)

عرض اتحاد طلاب الهوسا في جامعة البحر الاحمر مكتبة الهوسا ( كتاب الله مترجم باللغة الهوساوية و كثير من الكتب الاسلامية مترجمة بلغة الهوسا + ادوات العلاج البلدي ( دواية / توادة , القلمي , لوح / اللو و جزء من العشاب اشهرهم ققي و هو نوع من العشاب لعلاج البوز الجنسي
طلاب الهوسا في مهرجان جامعة البحر الاحمر
Sudanese Hausa students in university Red Sea Festival

طلاب الهوسا في مهرجان جامعة البحر الاحمر
Sudanese Hausa students in university Red Sea Festival


عرض ابناء الهوسا في دارفور ( نيالا) اداة الحرب في زمن المهدية و ما قبله ( كوري د بكا )
View Hausa people in Darfur (Nyala) tool of war in time of Mahdia and earlier (Cory d baKa)


عرض تراث الهوسا في كسلا
Sudanese Hausa symbol
 شعار الهوسا في السودان

الجمعة، فبراير 24، 2012

وصالٌ و إتصال !!! للشاعر احمد ابو ازاهر الهوساوي

الهوسَا يا عَلمُ الهُدَى ورُموزهُ وجذور شعبٍ طيب الأعراقِ

وراوائعُ الأزمان تعرف إرثهم قيمٌ تُجسدُ قمةُ الأخــــلاقِ

وهبوا النفوس بِطِيبِهَا لِطَبِيبَهَا لزموا الخشُوع لقاسم الأرزاقِ

هِممٌ لها في الشاهقاتِ مآذنٌ ورعٌ وزهدٌ خَافَــــــــهُ الإملاقِ *

فـــــالأرضُ طُهرٌ للعبادةِ موطنٌ والدِين في عُرف القبيلة باقِ

السبت، فبراير 18، 2012

مجموعة قرقاجيا للثقافة والتراث

dansudan
شهدت أمسية الجمعة 30/12/2011م وبأم بدة الحارة 43 ميلاد مجموعة قرقاجيا للثقافة والتراث حيث تم اعتمادها من قبل الفرقة القومية للفنون الشعبية التابعة للإدارة العامة للفنون بوزارة الثقافة الاتحادية ضمن منظومة الفرق والمجموعات التي تعمل في مجال الفنون الشعبية الأهلية. وتهتم هذه المجموعة بنشر ثقافة وتراث الهوسا والتعريف به. وتضم هذه المجموعة تسعة فرق تراثية تتناول كلها ثقافة الهوسا وتراثهم إضافة لقضايا بقية مكونات المجتمع. وهذه الفرق هي فرقة المحبة وفرقة قرقاجيا سمارن هوساوا وفرقة قرقن ذكرى (سفينة الذاكرين) وفرقة ولقيا (البرق) وفرقة كومي ربوني وفرقة وتا تافتو وفرقة كينوا وفرقة هسكي وفرقة أبكر أبو زيتونة إضافة إلى رابطة الشعراء التي تضم مجموعة من الشعراء بلغة الهوسا.
وكلمة «قرقاجيا» مقتبسة من لغة الهوسا وهي تعني التراث وكثيرون قد لا يعلمون أن الهوسا لغة شأنها شأن اللغات الحية في العالم كالعربية والإنجليزية والفرنسية وغيرها. وهي تمثل لغة التواصل الأولى لكل الشعوب التي تقطن في الرقعة الجغرافية التي كانت تعرف قديماً ببلاد السودان والتي تقع جنوب الصحراء الكبرى وتمتد من البحر الأحمر شرقاً وحتى المحيط الأطلسي غربا. كما تمثل لغة الهوسا أهم اللغات الإسلامية ويتحدثها بها أكثر من مائتي مليون شخص على مستوى العالم، وقد كتبت بالحرف العربي قبل أكثر من ثمانية قرون وألفت بها العديد من الكتب في شتى ضروب المعرفة وترجمت منها وإليها كتباً ومؤلفات عديدة كما تدرس بالعديد من الدول في جامعاتها ومعاهدها المختلفة وتبث بها العديد من البرامج عبر المحطات التلفزيونية والإذاعات العالمية.
إن كلمة هوسا - وكما ذكر البروفيسور يوسف الخليفة أبوبكر في مقال له نشر بصحيفة الرأي العام في أكتوبر من العام 2010م: «لم تعد تعني قبيلة الهوسا بل تتضمن كل من يتكلم الهوسا ممن ينحدرون من أصول مختلفة إلا أنهم صاروا هوساويين لغة وثقافة». ويعضد ذلك ما ذكره البروفيسور الأمين أبو منقة - وهو من أبناء الفولاني - حيث يقول: «تعتبر لغة الهوسا أولى اللغات التداولية في غرب أفريقيا حيث يتحدث بها أكثر من ثمانين مليون نسمة ينتمي كثير منهم عرقاً إلى قبائل أخرى غير هوسية تهوَّست عبر العصور وصارت لا تعرف لها هوية غير هوية الهوسا، لذلك بدأ الباحثون منذ فترة بالتعامل مع الهوسا باعتبارهم أمة مثل الأمة العربية قد تعدت مرحلة القبيلة وليسوا بقبيلة».
إن الهوسا يعتبرون من ضمن مكونات المجتمع السوداني ويمتلكون إرثاً ثقافياً كبيراً وتراثاً ثراً وغنيا، ومع هذا لم يكن هذا التراث وهذه الثقافة بمعروفين لدى السواد الأعظم من أفراد الشعب السوداني وذلك بسبب الربكة التي أحدثها اسم «الفلاتة» الذي يطلقه الشعب السوداني كاسم جامع ليضم كل القبائل السودانية التي تعود بجذورها إلى غرب إفريقيا وأهمها وأكبرها الهوسا وإن كان اسم «الفلاتة» هو في الحقيقة اسم لإحدى هذه المجموعات القبيلة وهم «الفلاني» كما يعرفون بهذا الاسم لدى الهوسا بينما يعرفون باسم «فلاتة» لدى قبائل الكانوري عند بحيرة تشاد. وفي ذلك يقول البروفيسور يوسف الخليفة أبوبكر في مقاله آنف الذكر: (لم يختلف الناس في أسماء إفريقية كاختلافهم في قبيلة ولغتهم)، (ولذلك يكتنف الغموض لدى العامة والخاصة في مفهوم الفلاتة). ويعضد ذلك الدكتور عمر عبد الماجد في كتابه (تاريخ الدول والإمبراطوريات الإسلامية في السودان الغربي والأوسط)؛ حيث يقول: (ولعله من المفيد أن نؤكد في البدء بأن الأسماء التي تطلق على هذه المجموعة الإثنية تختلف من مكان لآخر فهم يعرفون باسم «الفلاني» في ديار الهوسا وباسم «الفلاتة» في ديار الكانوري عند بحيرة تشاد وباسم «بني فلان» لدى القبائل العربية والبربرية في منطقة تمبكتو وباسم «بولي» لدى علماء الأجناس الفرنسيين. أما الفولاني فإنهم يطلقون على أنفسهم اسم «فولبي» بل حتى أصلهم الذي ينحدرون منه وكما ذكر الدكتور عمر الماجد لا يزال لغزاً من ألغاز التاريخ الأفريقي إذ أن هناك العديد من الفرضيات في هذا المجال ويتفق معه البروفيسور الأمين أبو منقة في هذا الزعم؛ حيث أشار إلى وجود ما لا يقل عن عشر نظريات حول أصلهم.
بسبب هذه الربكة التي أحدثها هذا الاسم فقد ضاعت كل إسهامات الهوسا الثقافية وحجبت معظم أعمالهم التراثية عن الأسماع والأنظار بل منها ما نسبته بعض القبائل إليها وحتى تاريخهم المشرق بالسودان وإسهاماتهم منذ المهدية بل حتى قبلها وإلى ما بعد الاستقلال لا تزال مجهولة هي الأخرى، لذلك وحتى يرد الفضل إلى أهله ويتعرف الناس على الهوسا وإسهاماتهم في شتى المجالات جاءت مجموعة قرقاجيا للثقافة والتراث لتتحمل عبء التعريف بهذا التراث وتوثيقه وحفظه للأجيال القادمة.
وبما أن مجموعة قرقاجيا للثقافة والتراث تهتم بنشر ثقافة وتراث الهوسا إلا أنها وبحكم أن الهوسا جزء لا يتجزأ من مكونات الشعب السوداني فسوف تهتم هذه المجموعة في أعمالها التي سوف تقدمها بكل قضايا المجتمع بمختلف تكويناته لأنها تأثرت بهذا المجتمع وأثرت فيه، لذلك وبالرغم من خصوصية الاسم إلا أنها سوف تنظر إلى الجميع نظرة واحدة وتحقيقاً لذلك فإنها تسعى إلى تحقيق حزمة من الأهداف السامية والغايات النبيلة التي يمكن تلخيصها في الآتي:
1- نشر تراث وثقافة الهوسا والتعريف به.
2- الحفاظ على ثقافة وتراث الهوسا وذلك بتسجيله وتوثيقه.
3- تشجيع الانفتاح الثقافي والتواصل التراثي بين قبيلة الهوسا والقبائل المختلفة لتقوية أواصر الترابط والتآخي بين مكونات المجتمع.
4- نشر ثقافة السلام والتعايش السلمي بين مكونات المجتمع المختلفة.
5- المساهمة في التعبئة العامة للمشاركة في القضايا القومية والوطنية.
6- المساهمة في محاربة التمييز العرقي والاستعلاء القبلي والجهوي وترسيخ معاني الوحدة الوطنية.
7- إحياء روح التكافل والتراحم بين أفراد القبيلة وترسيخ مبادئ العدالة والمساواة بين مكونات المجتمع المختلفة.
8- المحافظة على النظام العام وصون المجتمع من التمزق والتفسخ والانحلال وذلك بتزكية القيم الروحية الفاضلة ومحاربة العادات الضارة.
أما الأساليب والوسائل التي سوف تستخدمها المجموعة لتحقيق هذه الأهداف وإنزالها لأرض الواقع فهي سوف تستخدم كل الوسائل المتيسرة التي لا تتعارض مع القوانين والأعراف السائدة بالمجتمع ويمكن تلخيص هذه الوسائل في الآتي: -
1-إحياء الحفلات الشعبية في المناسبات المختلفة لعكس ثقافة وتراث الهوسا.
2- تسيير القوافل الثقافية بالتعاون والتنسيق مع بقية قطاعات المجتمع للتعريف بتراث وثقافة الهوسا.
3- إقامة الأسابيع والمهرجانات الثقافية بصورة دورية وفي مناطق السودان المختلف.
4- المشاركة في إحياء المهرجانات الثقافية والتراثية داخلياً وخارجيا.
5- المشاركة في إحياء المناسبات القومية والتعبوية.
6- إقامة المعارض والندوات والمحاضرات للتعريف بتراث وثقافة الهوسا.
7- التعاون مع كل الجهات التي تعنى بنشر الثقافة والتراث داخليا وخارجيا.
8- استخدام كل وسائل التكنولوجيا المعاصرة لنشر وتوثيق تراث وثقافة الهوسا والتعريف به.
9- إصدار المطبوعات والمجلات والمشاركة في المطبوعات والمجلات والصحف للتعريف بثقافة وتراث الهوسا وتوثيقه.
انعقدت الجمعية العمومية لهذه المجموعة وتم اختيار الأستاذ/ عبده مصطفى داؤود رئيساً لها والأستاذ/ إدريس أبكر أبو زيتونة أميناً عاما، إضافة إلى ثمانية وعشرين عضواً آخرين لعضوية المكتب التنفيذي الذي يضم عشر أمانات، كما تم اختيار الأستاذ/ أبكر أبو زيتونة رئيساً فخرياً وراعياً للمجموعة.

السبت، يونيو 25، 2011

ملامح من تاريخ وثقافة الهوسا في السودان






تعتبر قبائل الهوسا من القبائل الكبيرة في السودان، وقد انتشرت في جميع المدن والقري السودانية بفضل انفتاحها ومصاهرتها للقبائل السودانية المختلفة
و تعتبر لغة الهوسا من اكبر لغات افريقيا عدد المتحدثين بها لا يقل من 250 مليون شخص في القارة السمراء
بالاصافة الى 8 مليون في سودانا الحبيب و هذه اللغة تكتب بالحروف اللاتينية و العربية وتبث اخبارها عبر الإذاعات العالمية المتعددة وإذاعة الوحدة الوطنية بأم درمان. الهوساوي السوداني إنسان جاد وعملي ويتفاعل مع الحراك الاقتصادي لاسيما في التنمية الزراعية وقد عرف الهوسا بحبهم وتمرسهم على الزراعة في كل حقول المشاريع الزراعية الرائدة التي نشأت في السودان- وقد عرف الهوسا بالجد وقوة التحمل والصبر في العمل الزراعي أو الصناعي أو المهني أو التجاري. و الانسان الهوساي " يميزهم الصلاة والصوم ومعظم الهوسا يتبعون الطريقة التجانية
يتواجد الهوسا على ضفاف نهر عطبرة والرهد وينتشرون في القلابات وريفي كسلا وغرب القاش وفي أروماتي وفي ود الحليو وفي سنار ومايرنو وفي الدمازين والروصيرص وأرياف الجزيرة "مشروع الجزيرة" ودلتا طوكر والقضارف ومشروع المتمة. وقد انتشرت الهوسا في الولايات الجنوبية المختلفة وأعالي النيل في ملكال وفي بحر الغزال وقد استفاد على بلدو مدير المديرية الاستوائية "من الفريني خاصة الهوسا" في نشر الدين الإسلامي وسط الجنوبيين وتم إنشاء "82"خلوة منها عشرون خلوة للسلاطين في ياي والبقية في جوبا وتوريت ويامبيو وإنزارا ومريدي ومسجد في كبويتا.
ورغم أن مرسوم المناطق المقفولة عام 1920م، الذي هدف إلى عزل جنوب السودان غير المسلم عن شماله المسلم يقضي من ضمن سبل إنفاذه لترحيل الهوسا والفلاتا والتجار العرب في الجنوب والخوف من وجود الهوسا في راجا وواو وبالرغم من ذلك فإن وجودهم لازال ملموساً ومؤثراً. وتقول بعض الوثائق من دار مساليت "لقد لعب العمدة حامد محمد عثمان الهوساوي دورا عظيماً وخالداً في تاريخ سلطنة المساليت في الجنينة". ويقول المساليت هذا الرجل وقف معنا في حريتا ضد الفرنسييين في دوريني وكرندنق ودرجيل "السلطان عبد الرحمن بحر أبكر إسماعيل".
وفي المهدية برز أمراء الهوسا منهم الفكي مندي أبو دقن الهوساوي والقائد أبو التيمان الذي قاد حلف المسراب بالعباسية تقلي في جبال النوبة وهو الحلف الذي قدم الدفعة القوية لانتصارات المهدي.
*الهوسا في الخرطوم
بدأت نجميات الهوسا في
مناطق عديدة في الخرطوم بدأت تجمعها في منطقة المقرن ثم إلى جوار مسجد الخرطوم الكبير ثم إلى جنوب كبري المسلمية في أواخر الستينات ثم إلى ديم سلك وديم الزبير وفي عام 1943م، رحل المواطنون بعد التوزيع إلى حي الزهور "الزهور فتحت- بالخرطوم وظلوا قرابة العشرين عاماً ، و ايضا كانوا من اغلب سكان عيشش فلاتة منذو زمن بعيد تقرر ترحيل ذلك المخيم الذي عرف بـ"عشش فلاتة" إلى الجنوب الشرقي من ميدان السباق بواسطة مكتب الأراضي التابع لمديرية الخرطوم، لقد هدمت "880"عشة في المنطقة وأقيمت أخرى جديدة وتم ترحيل "160"عائلة من قبيلة الهوسا ضمن القبائل الأخرى التي رحلت، وفي مطلع التسعينات تم ترحيل تلك المنطقة إلى جنوب الصحافة "الإنقاذ" وأصبحت الإنقاذ من الأحياء الممتازة في الخرطوم الآن من ناحية التخطيط والخدمات ويسكن غالبية الهوسا هناك والإنقاذ مربع "2"وقد ضم نظامهم الأهلي أكثر من ثلاثين عمدة وشيخاً بمحلية حي النصر شأنها شأن المحليات الأخرى.
وايضاً هناك وجود للهوسا في محليات أم بدة وأم درمان وكرري والفتيحاب والريف الجنوبي وأصبح فريق الهوسا في أم درمان هو حي العباسية شرق الآن تحت زعامة الأستاذ إبراهيم هارون محمد قوبراوي وقدح الدم والشيخ إبراهيم ناصر "مرفعين الفقراء".
تراث الهوسا زاخر بالفنون المختلفة.. وهم مميزون بالفن والغناء والموسيقي من خلال فرق الفنون الشعبية والكيتا وبعض الجماعات الغنائية والرقصات الشعبية المصاحبة لها والغناء عند الهوسا متميز من حيث اهتمامه بالقيم النبيلة ونشر الفضيلة والخير والأمن والسلاح وبروز دور المعاني تأصيلاً في التوحيد والأمر بالمعروف والنهي عن المنكر فلا نجد أغنية من أغاني الهوسا إلا ويذكر فيه اسم المولي عز وجل واسم النبي صلى الله عليه وسلم، وتشجع أغاني الهوسا إلى العلم والإنتاج وغرس بذور المحبة والمودة وذم الكسل ولعب الميسر وشرب الخمر والتمجيد "إيكي" ومن أشهر أغاني الهوسا التي تدعو إلي العمل أغنية:"تاريلو تاريا ريا تاريلو ماتاتا كدنق كسلا سنغاري دكاكا مجي قرية كدنق قربا سنغاري دا دامنا مجي حلفا وسوكي يعني أن قروش كسلا لو انتهت وأصبح لا يوجد عمل بها نذهب إلى خشم القربة أو حلفا أو السوكي.
ومن أشهر فنون الهوسا آلة الكيتا بالرغم من أنهم نقلوها عن البرنو بالاضافة إلى آلات موسيقية أخرى منها آلة القورمي الوترية ثم آلة القراية ثم مجموعة كلنقو الايقاعية وآلة كاكي ثم آلة بمبرو وإيقاع الطبل والدف ويسمي "تمبري". ومن أشهر فناني الهوسا المعلم والمربي موسى أحمد يحيي والد الفنانة عائشة الفلاتية- والفنانة عائشة الفلاتية وشقيقتها عازفة العود جداونة موسى. ومن أشهر الأغنيات للهوسا أغنية سماري وتعني الشباب وجمعية سماري للآداب والفنون "معناها جمعية الشباب".
داكي سماري؛ بين الشباب وأغنية سماري غنتها عائشة الفلاتية عند الاحتفال بعيد استقلال دولة نيجيريا وغنت عائشة الفلاتية أيضاً أغنية "الله بادتق حليبا" وغنى إبراهيم حسين أيضاً أغنية سماري- وغنت سمية حسن أيضاً بلهجة الهوسا. ونذكر بعض فناني الهوسا أمثال الفنان إسماعيل محمد- الفنان داؤود خليل- الفنان الأمين جبريل جركانة- سليمان سند- ومن كسلا عنتر هوسا وفاطمة هوسا من حلفا






الأربعاء، مايو 18، 2011

أمة الهوسا أفيقوا وأستفيقوا

مة الهوسا أفيقوا وأستفيقوا

موقع لغة الهوسا اكتسَى أجملُ حُـــــــــــــلَّة نَرجَسّيُ اللَّونِ كَالــَّروضِ المُطِّلةْ
فَلنَكُن للَّروضِ زهرٌ وربيـــــــــعٌ وخريفٌ قادمٌ مِـن خَّير مِــــــــــلَةْ
من سِوانَا سَوفَ يَثْرّي موقع لغة الهوسا؟ مَنْ سَيَحْمِي إرْثَنَا فِي كُــلِّ حِـــــلًةْ
إعْلـَـــمُوا يَا مَنْ تَناسَو مُلـتَقَانَا لَنْ تنَالُوا المًجّدً أشْـــتَاتًا وشُـلةْ
إنـــمَا المجدُ نضالٌ وإتــــــحادٌ إن أبَيْــتُم ، تلك واللَّـهِ لَعِلّةْ
ثَورةُ الأقْلام قَد دَّارَتْ رحـَــــاهـَـا جَنّدُوا التَّعــبِيَر كلمَاتٌ وجُمـــلَةْ
أطلقُوا الأحْرفَ فَالدُنيَا كِــتابٌ يَحْــتَوّي الأحْدَاثَ ، والكونُ كُتـْـلَةْ
امةُ الهـوسَا أفيـقُوا واسْتَــــفِيقُوا قد مضَى عَهدُ الشِعاراتُ المُمِــلةْ
لا تُقــــــولوا إننـَا كُـنا وكـنا إنمَا الــماضِي جِراحَاتٌ وذّلــــــةْ
هــــذه الأنـفاقُ قد طال مداهـــَـا أخرجوا منها بشمعاتٍ وشُعـــــلةْ
أحرقُـــــوا ما كان بــــالأمسِ وباءٌ من خُــــنوعٍ وخُضـوعٍ للجِبِلّةْ
زَرَعُــــــوا الإحْـــباطَ فينّا بالتّبنِـي وتوارَوْا خلفَ أسوار الأدلـِـــةْ
اِستبَاحونا وبَاعُــــوا مِـــــــنْ دِمَانَا فّي مزَادِ العُمر في أسوأ رِحــلةْ
وأقامُـــــوهَا سَراديبَ عَـــــــــزاءٍ هَـا هِيَ الأيَامُ دارتْ للأخِـــلةْ
فَلنكُن للــخيرِ عَـــــونٌ لا نُـــبالي إنـــــنَا رمزٌ لمِــيقَاتُ الأهِلّةْ
إنما الآمال مـــرآة السـجايـــــا والتمني يورث الهمة غـــفلة
أدفنوا الآهات واْسقُوهَا طُمُوحــًــا مِـن نُفوسٍ راضِـــياتٍ مُسـتقِلَةْ
اكظُّمُوا الغّــيظَ لِنمضِــي للأعَالِي وَلْنـَـكُن رمزًا كَمَا كُنَا كَـــنَخْلَةْ
نَخلةٌ تُرمَى مِنّ الــــرَّامِي مِــرَارًا مِن ضَعيفٍ جائٍع لنْ نستَــــــــغّلهْ
إنْ عَقَدنَا العَزمَ حَتمًا سوَف نسمُو إنَـمَا العَاقِـــلُ مَن يسمُو بعَقْلهْ
أمةُ الهـوسَا أنِيـــرُوا وَاسْتَــــنِيرُوا إنـــكُم شعبٌ ولودٌ غَيرُ قِـــــلةْ
أطلبُــــوا العِلمَ غـــــداةً ورواحًــــا مِن بِلادِ الصِّينِ أومِن أرضُ دِجْلَةْ
إنَمَا بالعِــــلمُ يُشْرَى كلُ عِـــــــــزٍ فشريف القوم ليس من يملك عُمْلة
فاستَعِــــينُوا با لله وبِالصَّبرْ تَفُوزًوا وَاْجعَلُوا العَالِمَ عُـنْوانَ التَجِّلَـــة

الأحد، مايو 08، 2011

Takaitacan tarihin marganyi Osama Ben Ladan

An haifi Usama Bin Laden a ranar 10 ga watan Maris na shekarar 1957 a birnin Riyad na kasar Saudiya .
A 1988 ya kafa kungiyar alka’ida inda ya taimakawa dakarun neman yanci kan mamayen da kasar tarayyar Soviyat ta yiwa kasar Afghanistan.


A 1992 zuwa ta 1996 ben laden ya fara cacakar gwamnatin kasar Suadiya da ta baiwa dakarun kasar Amurka damar yin amfani da kasar ta wajen tada yakin Golf na 1990 zuwa ta 1991. Ya yi gudun hijira ya bar kasar ta saudiya.


A shekara ta 1996 bin Laden ya tare a kasar Afghanistan karkashin mulkin ‘yan taliban, a ranar 7 ga watan Ugusta na shekara ta 1998 Alka’ida ta kai hari a kan ofisoshin jakadancin amurka a Kenya da Tanzaniya inda mutane 200 suka mutu,


a ranar 11 ga watan septemba na shekara ta 2001 harin da alka’idar ta kai a kan ‘yan tawayen benayen cibiyar hada-hadar kasuwanci ta duniya a birnin New York ya yi sanadiyar mutuwar mutane dubu 3.


A nan take kasar Amurka ta zargi kungiya inda ta kaddamar da hari a kasar Afghanistan wanda ya haifar da faduwar gwamnatin Taliban, Ben Laden ya tsere a kasar Pakistan mai makwabtaka da Afganistan kafin ya cimma wa’adinsa a ranar 1 ga wannan wata na Mayu a garin Abbottabad (Pakistan) a karakashin harin da dakarun Amurka suka kai masa.

الاثنين، مايو 02، 2011

An kashe Osama bin Laden



Usama Bin laden da AymanAlzawahir da Muhammad Atef

Usama Bin laden da AymanAlzawahir da Muhammad Atef


Jami'an gwamantin Amurka sun ce, an kashe shugaban kungiyar Al-Qaeda, Usama bin Laden, kuma Amurka ta samu gawarsa.


Dakarun Amurka dai sun jima suna farautar Osama bin Laden, tun ma kafin harin sha daya ga watan Satumbar 2001, lamarin da yayi sanadiyyar mutuwar kusan dubu uku.


Wakilin BBC ya ce: "A matsayinsa na wanda ya kafa kungiyar Al-Qaeda, kuma yake jagorantarta, Usama bin Laden ya kasance sananne a duniya, inda wasu a kasashen yammacin duniya ke kallonsa a matsayin tushen ta'ddanci.


Shugaba Obama wanda ya sanar da kashe Usama ya ce, kisan nasa ya biyo bayan fafatawar da aka yi ne, kuma tuni Amurka tana rike da gawar sa.


Ana zargin Usama da aikata manyan laifuka a sassa dabam-daban na duniya ciki har da harin sha daya ga Satumba da aka kai kan tagwayen gine-ginen cibiyar kasuwancin duniya dake New York a kasar Amurka.


Shi ne dai babban mutumin da Amurka ke nema ruwa a jallo.


Tuni dai kasar Amurka ta sanya ofisoshin jakadancinta a kasashen duniya cikin shirin ko ta kwana.


Mutane da dama ne suka taru a gaban fadar White House da ke Washington DC suna ta nanata kalmar "USA, USA" bayan an samu labarin mutuwar Usama.


Hari kan harabar gidan da yake ciki


Harin Sha daya ga Satumba

Harin Sha daya ga Satumba


Shugaba Obama na Amurka ya ce an bashi labari a watan Agustan da ya gabata cewa akwai yiwuwar a samu bayanan inda Usama Bn Laden yake.


Yace a lokacin babu tabbaci, hakan ya sa suka shafe watanni suna bibiyar bayanai.


"Na gana a lokuta da dama da masu bani shawara kan al'amuran tsaro, kuma muka yi ta tattara bayanai a kan yiwuwar mun gano inda Bin Laden yake boye can cikin harabar wani gida dake can cikin kasar Pakistan. In ji shugaba Obama na Amurka.


Ya kuma kara da cewa: " Daga karshe a makon da ya gabata, na yanke cewa mun samu isassun bayanai da za su sanya mu dau mataki, don haka na bada umarnin a kamo Usama don hukunta shi.


Kuma ranar Lahadi, wasu dakarun kasar Amurka suka kai hari a Abbottabad kimanin kilomita dari arewa maso gabashin birnin Islamabad.


Bayan 'fafatawa' an kashe Bin Laden, kuma sojojin Amurka na rike da gawar sa, in ji shugaba Obama.


Jirgin Amurka daya dai ya rikito a lokacin harin.


An kashe wasu karin mutane uku a harin, ciki har da dan Usama bin Laden din da kuma wata mata yayinda aka ji wa wasu matan biyu rauni.


Usama


Mutane da dama na murnar kashe Usama a Amurka

Mutane da dama na murnar kashe Usama a Amurka


Sunan Osama Bn Laden, mutumin da ya kafa kungiyar Al-Qaeda ya zama ruwan dare gama duniya, a cikin shekaru da dama.


A wajen mutanen da ke yammacin duniya, abin da yake fara zuwa a ransu idan an ambaci sunan Usama shi ne, ta'addanci, kasancewa ana yi masa kallon mutumin da ya dauki nauyin kai hare-haren ranar 11 ga watan Satumbar shekarar 2001.


A wajen wadansu kuwa, Usama cikakken musulmi ne, wanda ya kaddamar da jIhadi kan kasashen yammacin duniya.


Usama Bn Ladan, wanda mahaifinsa wani attajiri ne, mai kamfanonin gine-gine, ya girma cikin jin dadi.


Sai dai jim kadan bayan da tarayyar Soviet ta mamaye Afghanistan, sai Usama ya shiga kungiyar mujahideen da ke kasar, inda suka fafata da dakarun tarayyar Soviet din.


Kuma tun daga nan ne ya kafa kungiyar Al-Qaeda.


Bayan ya dawo Saudi Arabia ne dai, ya fara caccakar shugabanninta, wadanda ya ce sun kyale Amurka ta shiga kasar.




Labarin kisan Usama abu ne mai kyau, sai dai irin martanin da mutane ke mayarwa babu dadin ji, musamman tsalle da murnar da mutane ke yi a kewayen fadar White House ta Amurka.


Justin King


Ya ce sun yi hakan ne, da zummar ganin sun kawar da dakarun Saddam Hussain daga Kuwait.


A shekarar 1998 ne dai Usama Bn Laden ya ayyana yaki kan Amurka.


Kuma a shekarar ne dai, kusan duk manyan kasashen duniya suka amince cewa shi ne mutumin da ya bayar da umarnin kai hari a ofisosnhin Amurka da ke gabashin Afurka.


A shekarar 2000, kungiyarsa ta Alqaeda ta yi rugu-rugu da wani jirgin yakin Amurka, sannan daga bisani, kungiyar ta kai hare-hare a biranen New York da Washington, a shekarar 2001.


Kuma duk da dala miliyan 27 da Amurka ta sanar ga duk wanda ya taimaka aka kama shi, Usama Bn Ladan ya ci gaba da zulle mata, inda ya kasance a boye, a wadansu yankuna masu cike da tsaunuka dake kan iyakar Afghanisatan da Pakistan.


Martani


Shugabannin siyasa da sauran al'ummomin duniya na ci gaba da bayyana ra'ayoyinsu dangane da kashe jagoran kungiyar alka'ida Usama bin Laden.


Tsohon shugaban Amurka George Bush, ya ce wannan gagarumar nasara ce ga Amurka, ga mutanen da ke neman zaman lafiya a sassa dabam-daban na duniya, da ma wadanda suka rasa rayukansu a harin ran sha daya ga Satumba.


Shi ma tsohon shugaban Amurka Bill Clinton ya ce, wannan batu ne mai matukar muhimmanci ba wai ga iyalan da suka rasa wani nasu a harin sha daya ga Satumba ba, da ma sauran hare-haren da kungiyar Alqaeda ta kai, amma ga mutanen duniya baki daya wadanda suke son gina makoma ta zaman lafiya ga duniya.


Fira Ministan Burtaniya David Cameroon, ya ce labarin mutuwar Osama bin Laden za ta kawo saukin lamari ga al'ummar duniya.



Usama a cikin wani kogo a shekarar 1998

Usama a cikin wani kogo a shekarar 1998


Fira Ministan Israela Benjamin Netanyahu, na da ra'ayin cewa, wannan gagarumar nasara ce da kuma 'yanci, da kuma tsari na kasashen da ke amfani da demokradiyya wajen yakar ta'addanci kafada-da-kafada.


Shi ma Fira ministan kasar Kenya Raila Odinga, ya shaida wa BBC cewa babbar nasara ce a yakin da ake yi da ta'addanci.


Shi ma Fira Ministan New Zealand John Key, cewa ya yi Osama shi ne ya yi sanadin mutuwar dubban mutane, ciki har da 'yan kasar New Zealand a sassan duniya.


A nata bangaren, ma'aikatar harkokin wajen India cewa ta yi, ya kamata duniya ta kara azama wajen karfafa hadin kanta a yaki da ta'addanci.


Shi kuwa wani mazaunin birnin New York na kasar Amurka Justin King a sakon da ya aike wa BBC cewa ya yi, labarin kisan Usama abu ne mai kyau, sai dai irin martanin da mutane ke mayarwa babu dadin ji, musamman tsalle da murnar da mutane ke yi a kewayen fadar White House ta Amurka.

الثلاثاء، أبريل 19، 2011


Nuhu Ribadu

Nuhu Ribadu ya yi alkawarin kafa sabuwar Najeriya


An haifi Malam Nuhu Ribadu a ranar 21 ga watan Nuwamban 1960.


Ya samu shaidar digiri ta farko a fannin ilimin shari'a daga jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a 1983.


Ya kuma karbi shaidarsa ta zama lauya a shekara ta 1984.


Malam Nuhu Ribadu ya kara halartar jami'ar Ahmadu Bello domin karatun digiri na biyu a fannin na shari'a.


Sannan ya halarci sashin kasuwanci na jami'ar Harvard da ke Amurka.


Daga nan ne kuma ya fara aiki da Hukumar 'yan sandan Najeriya, inda ya ci gaba da aiki a matakai daban-daban, har ya zamo shugaban bangaren shari'a da gabatar da masu laifi a ofishin Hukumar da ke Abuja.


Shekaru 18 din da ya shafe yana aiki a Hukumar 'yan sandan Najeriya, ya kai har aka nada shi shugaban Hukumar yaki da yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati (EFCC) a watan Afrilun shekara ta 2003.


Yana cikin kwamitin tattalin arziki da shugaba Obasanjo ya kafa a shekara ta 2003 zuwa 2008, wanda ya haifar da sauye-sauyen da aka gudanar a bangarori daban daban na kasar.



Malam Nuhu ya bayyana aniyarsa ta tsaya wa takarar shugaban kasa a zaben da za a yi a watan Afrilu karkashin jam'iyyar adawa ta ACN a a watan Disambar 20101



Nasarar da ya samu ta hadar da cire Najeriya daga jerin kasashen da ba sa bada hadin kai ta fuskar yaki da cin hanci da rashawa.


A watan Oktoban 2007 ne kuma tsohuwar gwamnatin shugaba Umaru 'Yaradua ta cire shi daga shugabancin Hukumar ta EFCC, sannan aka tura shi ya karo karatu.


Mallam Ibrahim Shekarau



An haifi Shekarau ne a unguwar Kurmawa da ke jihar Kano, Ya kuma yi karatun Firamare a makarantar Gidan Makama daga shekarar (1961-1967).


Ya yi karantun sakandare a Kano Commercial College daga shekarar (1967-1973) sannan kuma ya garzaya jam'iyyar Ahmadu Bello da ke Zaria daga shekarar (1973-1977) inda ya samu takardar shaidar digiri ta farko.


Bayan da ya kammala karatunsa na jami'a, mallam Ibrahim Shekarau ya yi aikin gwamnati, sannan ya koma dakin karatu inda ya zama malamin lissafi a Government Technical College da ke Wudil a shekarar 1978, bayan shekaru biyu ne kuma ya zama shugaban makarantar Government Day Junior Secondary School a Wudil.


A shekarar 1980 an koma da shi makarantar Government Secondary School da ke Hadejia, sannan Government College Birnin Kudu a 1986, sai kuma Government Secondary School a Gwammaja da kuma makarantar Rumfa College a 1988, duk a matsayin shugaban makaranta.


Daga nana dai mallam Shekarau ya zama mataimakin darakta a harkar illimi a shekarar 1992, bayan kuma shekara guda aka mayar da shi darekta.


Daga nan dai likkafa ta ci gaba inda ya zama babban sakatare a ma'ikatar harkar illimi.


A watan Fabrerun shekarar 2000, malam Shekarau ya koma aikin gwamnati, kafin a koma da shi kwalejin share fagen shiga jam'ia a matsayin babban malamin lissafi.


A nan dai Shekarau ya ajiye aiki da gwamnati bayan ya yi aikin na tsawon watanni 17 a kwalejin.


Siyasa


Ba'a dauki Malam Ibrahim Shekarau a matsayin wani dan takara da zai yi tasiri ba a zaben gwamnan da aka yi a shekarar 2003 a jihar, amma daga baya kuma sai ya yi tasiri inda ya lashe zaben.


Kuma Malam shekarau ya kafa tarihi inda ya zama gwamna na farko da aka zabe shi a karo na biyu a matsayin gwamna a jihar Kano.


Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero, ya nada shi a matsayin Sardaunan Kano a karon farko a tarihin masauratar Kano.


Malam Ibrahim Shekaru ne dai dan takarar shugaban kasa, karkashin inuwar jam'iyar ANPP a Zaben watan Afrilu na shekarar 2011.

Takaitaccen tarihin janar Mohammadu Buhari

Janar Mohammadu Buhari







dansudan

An haifi Janar Muhammadu Buhari ranar 17 ga watan Disambar shekarar 1942, a garin Daura.
Tauraruwar janar Buhari ta fara haskawa a lokacin da aka bashi mukamin ministan man petur da ma'adanai a shekarar 1975, a zamanin mulkin sojin janar Olusegun Obasanjo.
Ko da yake kafin nan shi ne gwamnan sabuwar jahar Arewa maso Gabas da janar Murtala Ramat Muhammed ya kirkiro.
Daga bisani kuma aka nada shi shugaban hukumar NNPC wadda aka fara kafawa a shekarar 1977.
A zamanin mulkin Janar Sani Abacha an nada shi shugaban hukumar PTF wadda aka kafa da kudaden rarar man da kasar ta samu a wannan lokaci domin gudanar da ayyukan ci gaban al'umma.
Kuma ayyukan da janar Buhari yayi wa Najeriya kama daga hanyoyi, asibitoci zuwa makarantu yasa wasu 'yan Najeriya son ganin ya sake zama shugaban kasar.
Sau biyu janar Muhammdu Buhari yana tsayawa takarar shugaban kasar karkashin tutar jam'iyyar ANPP wato 2003 da 2007, wadanda duka bai samu nasara ba.
Rashin nasarar da ya yi karo biyu bai sauya masa ra'ayi ba game da siyasa a Najeriya, kuma tuni ya kaddamar da tashi jam'iyyar da ya kira CPC wadda yake takarar shugaban kasa a zaben da za'a yi a shekarar 2011.

Takaitaccen tarihin Shugaba Goodluck Jonathan

Shugaba Goodluck Ebele Jonathan






An haifi Dr. Goodluck Ebele Jonathan ranar 20 ga watan Nuwambar shekarar 1957 a garin Otueke na karamar hukumar Ogbia dake a wancan lokacin yankin gabashin Najeriya, yanzu kuma yake jihar Bayelsa.


Iyayensa na sassaka jirgin kwale kwale ne.


Yayi karatun digirinsa na farko a fannin ilimin dabbobi.


Ya kuma yi digirinsa na biyu a fannin ilimin halittun ruwa.


Ya samu digirin digirgir a fannin ilimin dabbobi a jami'ar Patakwal.


Bayan da ya samu digirinsa na farko ya yi aiki a matsayin sipeton dake sa ido kan yadda malamai suke gudanar da ayyukansu, malamin jami'a da kuma jami'in dake sa ido kan kare muhalli, aikin da yake har zuwa lokacin da ya shiga siyasa.


A shekarar 1998 ne Dr. Goodluck Jonathan ya fara shiga al'amuran siyasa, inda ya shiga jam'iyyar PDP.


Ya zama mataimakin gwamnan jihar Bayelsa a shekarar 1999 bayan da Diepreye Alamieyesegha ya lashe zaben gwamnan jihar karkashin tutar jam'iyyar PDP.


Dr Goodlck Jonathan ya zamo gwamnan jihar Bayelsa bayan da majalisar dokokin jihar ta tsige Alamieyesegha bisa zargin kokarin hallata kudin haram a Burtaniya da kuma almundahana da dukiyar jama'a.


A shekara ta 2006 an zabi Dr. Goodluck Jonathan a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa, kuma bayan zaben da aka yi a shekara ta 2007 an rantsar da shi a matsayin mataimakin shugaba Umaru Musa 'Yar Adua.


Kamar ubangidansa Dr. Goodluck ya bayyana dukkan dukiyar da ya mallaka daga lokacin da ya hau kan mulki.


An rantsar da Goodluck Jonathan a matsayin mukaddashin shugaban Najeriya sakamakon rashin lafiyar da shugaban Najeriya na lokacin Umaru Musa 'Yar Adua ya yi fama da ita.


Bayan rasuwar shugaba Yar'Adua an rantsar da Goodluck Ebele Jonathan a matsayin shugaban Najeriya kuma babban kwamandan askarawan kasar.


Dr. Goodluck Jonathan na da mata daya Dame Patience Jonathan da 'ya'ya biyu.

الخميس، أبريل 14، 2011

KAMUSUN HAUSA

Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya Ta Jami'ar Bayero Ke Biya Hausawa


(Daga Bello Muhammad Danyaya)


Na jima ni kadai; ina ta tukuburi; ina cewa a raina; yaya malaman Hausa za su bar Hausawa cikin duhu game da sha'anin harshensu?


Sanin ma'anar kalmomin kowane harshe, shi ne mafi mahimmanci ga kowane dan harshen, da manazarci harshen, da ma bako mai sha'awar harshen.


Irin wannan abu ne ya sanya Turawa suka mayar da hankali da wuri, suka tattara kalmomin Hausa tare da fassara su cikin harshensu na Turanci, tare da buga abin, wanda muke kira kamus.


Tun a shekarar 1934 G.P. Bargery ya fitar da kamus dinsa mai suna Hausa-English Dictionary and English-Hausa Vocabulary (Oxford University Press, 1934).


Bayan wannan, a cikin shekarar 1962, wani Bature mai suna R.C. Abraham, ya fito da nasa kamus, wanda ya kira Dictionary of the Hausa Language (University of London, 1962).


Wadannan kamus-kamus biyu, su ne manya, kuma kansu ne aka dogara kan neman ma'anar kowace kalma ta Hausa. Duk da yake akwai wasu kamus-kamus din, wadanda ake amfani da su, amma dai wadanda aka ambata su ne manya.


Abin kulawa a nan shi ne, duk wadannan ayuka Turawa ne suka yi su.


Abin da kuma har yanzu ba a iyar da ganewa ba, shi ne, wadannan kamus-kamus da Turawa suka yi, sun yi su ne don taimakon Turanci da Turawa, da taimaka wa Bahaushe mai sha'awar Turanci.


Babu kome! Duk da haka wadannan kamus-kamus na Turawa, sun taimaka matuka, wajen adana wa Hausawa kalmomin harshensu, har zuwa yau (2007) da Allah Ya kaddari Malaman Hausa na Jami'ar Bayero suka fito da nasu kamus wanda aka yi don Hausa da Hausawa da mai sha'awar Hausa.


Tabbas, wannan kamus na Jami'ar Bayero ya zo daidai lokacin da ake matukar bukatarsa, a lokacin da wani abu wanda aka kira “Daidaitacciyar Hausa” yake neman halakar da mafi yawan kalmomin Hausa.


Daidaitacciyar Hausa, wani salo ne da ya cilasta yin amfani da karin harshen Hausa daya, tare da zabar wasu kalmomi wadanda za a yi amfani da su a rubuce-rubuce. Inda haka ke nufin wasu kalmomin ba a yarda a yi amfani da su ba. Inda haka zai yi sanadiyar barin amfani da wasu kalmomin Hausa dangurungum. A gaba kenan kalmomin harshen Hausa za su karanta, tunda wasu kalmomin an kashe su da karfi da yaji!


Alhamdu lillahi! Wannan kamus mai suna Kamusun Hausa ya tara wadannan kalmomi na Hausa, kuma daga kowane irin karin harshe na Nijeriyar Bahaushe. Kamus din ya tara tsofaffin kalmomi, da ma sababbi. Cikin tsari kamus din ya kasance, wanda zai burge kowa.


Ko ba a so, dole a ce wa mijin iya baba. Hakika duk yawan shekarun da aka diba, wajen samar da wannan kamus, da makudan kudin da aka kashe masa, da taron dangin da aka yi masa, kwalliyar da malaman suka yi masa, ta biya kudin sabulu.


A wani gefen kuma, wannan kamus ya kashe bakin tsanya; ya rusa duk wasu gunaguni masu fitowa daga irinmu, ‘yan-ga-mu-kashe-mu na Hausa!


Ina da kira! Kiran nawa shi ne, ya zama wajibi ga jami'o'i da cibiyoyi da kwalej-kwalej masu nazarin Hausa, su yi niya su mallaki wannan kamus.


Haka ma dakunan karatu, bai kamata su yi saku-saku da wannan garabasa ba.


Kai malamin Hausa da manazarci Hausa da mai sha'awar Hausa, ina ba ku shawarar, ku yi niya ku sami naku rabo. Ina yi maku gudun wannan kamus ya kare, ya zama ba a sami damar sake buga shi ba. Ku tuna Hausawa sun ce “Fara kamun safe”.


Ga mai bukatar wannan kamus mai suna Kamusun Hausa, zai iya tuntubar Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya ta Jami'ar Bayero, a ofishinta da ke harabar tsohuwar Jami'ar Bayero ta Kano. Kuma za a iya tuntubar ta, ta Jakar gidan waya. P.M.B 3011, Kano. Ko a lambar waya 060-317576, ko i-mel: csnlbuk@yahoo.com.


A cibiyar ana sayar da kwafin kamus din, a kan kudi Naira 2,000 mai makari mai kwari. Naira 1,500 mai makari mai taushi.